Gabatarwa: Dasunan Allah Mai
Rahama, mai jinkai, tsira da amincin Allah ya tabbata ga Ma'aikin Allah Annabi
Muhammad. Awannan lokacin da izinin Allah mai kowa mai komai muna fatan kawo
wadansu bayanaine na daban bayan kammala waccan doguwar salsala da take dauke
da wadansu abubuwa bakwai masu halakarwa. Wannan bayanai kuwa matashiyarsu
itace: Ibada Da Hukunci. Fatammu shine kawo bayanai filla-filla kan abinda ya
shafi hukunce-hukncen nau'ukan ibada kamar tsarki da rowan da ake tsarki da
shi, da kuma bayanai akan abinda yake najasa da alwala da abinda ke bata
alwalar ta taimama da wankan tsarki da abinda ke sa wankan, da huknce hukuncen
sallah, kamar sharuddan sallah lokutanta kiran sallah, salloli na farilla
nafilfili, tada ikama, kabaliyya da ba'adiyyah, hukunce-hukunce masallaci,
sallar kasaru. Hakanan muna fatan kawo bayan kan Azumi da Hajji d.s…gwargwadon
abinda Allah Ya hore, da fatan zamu tsaya musan Ibadar da Allah ya dora mana
kuma musan hukunce hukuncen wannan ibadar, Allah Ya yi mana jagora, amin summa
amin, asha karatu lafiya.
Ibada: Ma'anar ibada itace ''Gamamman sunane da ya tara
dukkanin abinda Allah yake so kuma ya yarda da shi, na zantuttukane ko na
ayyuka na filine koko na zuciyane''.
Kenan ibada tana shiga ayyukan
gabbai kamar: Alwala, zakka Hajji, kamar yadda maganama ke shiga cikin ibada
kamar: Karatun Kur'ani, Salati ga Ma'aikin Allah, na bayyane kamar tsarki dana
boye kamar niyya.
Hukunci: idan akace hukunci
shine hukunce-hukuncen da shara'a ta na cewa abu kaza: Wajibine, ko Haramunne,
ko kuma Mustahabbine ko Makaruhine, ko kumama Halasne. Wadannan abubuwa biyar su ake kira da Ahkamus
Shar'iyyah At-Takleefiyyah. Kuma ga bayanansu da Shara'a ta yi:
(1) Wajibi: Shine abinda ana
bada lada ga duk wanda ya aikata shi akan an'umarceshi, kuma ana azabtar da duk
wanda ya barshi. Kamar salloli na farilla da tsarki da Azumin Ramadan…'
(2) Haramun: Shine abinda idan
mutum ya aikata shi za ayi masa ukuba, idan kuma ya barshi yana da lada. Kamar:
Sata, Zina, Luwadi, Shangiya.
(3) Musthabbi: Shine idan mutum
ya aikata za'a bashi lada, amma idan bai aikataba babu komai akansa. Kenan
aikata shi ya fi. Kamar daga hunnuwa a lokacin kabbarar harama, kamar karatun
mamu alokacin da liman yake karatunsa aboye.
(4) Makaruhi: Shine abinda idan
an barshi akwai lada, idan kuma an aikata babu ukuba, kenan barinshi ya fi.
Kamar susa ana sallah da dan waige kadan.
(5) Halas: Shine abinda idan
an aikata babu lada akan aikatshin da aka yi, hakanan idan an barshi babu lada
akan barin na shi da aka yi, kenan sai an kallaci niyyar da tasa aka yi ko aka
bari akan haka za'a sami lada ko zunubi. Kamar bacci, idan mutum ya yi bacci da
wuri domin ya tashi cikin dare ya yi nafilfili da addu'oi to wannan yana da
lada, hakanan idan ya yi bacci domin yaba jikinsa hakkinsa, tunda yazo a hadisi
jikinkama yana da hakki, to duk wadannan akwai lada. Idan kuma mutum ya yi
bacci alokacin da yasan indai ya yi bacci a wannan lokacin took zai iya rasa
sallah to ba'ayarda ya yi bacci a wannan lokacinba, shi yasa aka hana bacci
tsakanin Magariba da Lisha.
Wadannan sune hukunce hukunce da sune ake hukunci, kuma tananne ake
kaiwa inda za'a yi hukunci akan ibadar mutum ta yi ko bata yi ba, kenan dole mu
tashi tsaye musan yadda za mu yi ibadarmu yadda Mahaliccimmu ya umarcemu mu yi
ta harshen Annabinsa Annabi Muhammad -Tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi-, ka da mu yi sakaci mu da iyalammu da kannemmu da yayyammu… Allah ya yi
mana jagora amin.
Lalle tsayawa akan a fahimci wannan addini na musulunci yana cikin
mafiya kyawun ayyukan da Allah ke so, kuma alamace ta Allah na son mutum da
alheri, kamar Yadda Ma'aikin Allah -Tsira da amincin Allah su tabbata a gare
shi- yake cewa ((Duk wanda Allah yake nufinshi da alheri sai ya fahimtar da
addi)). Bukhari ya ruwaitoshi a hadisi na:71, Muslim kuma: 1027.
Allah madaukakin sarki yana cewa: ''Shine
wanda Ya aiko manzonsa da shiriya da kuma addinin da yake na gaskiya''
Suratut- Tauba: 33. Shiriyar Itace ilimi mai anfani, Addini na kwarai kuwa
shine: Ayyuka masu kyau.
Babu wata tantama tabbas yakama kafin mutum ya himmatu wurin aikata
kowanne irin aiki yasan hanyar day a kamata yabi domin aikin na shi ya zama ya
yi shi daidai, ta yadda zai yi ya sauke aikin da aka dora masa wanda zai zama
sanadiyyar tseratar da shi daga wuta da kuma shigarshi aljanna.
Akan Haka Mutane
Sun Kasu Kashi Uku:
(1) Wadanda suka hada ilimi mai
anfani da kuma aiki na kwarai. Wadannan sun rabauta duniniya da lahira, don
Allay ya yarda da su.
(2) Wadanda suka san ilimi mai
anfani amma basu yi aiki da shiba, wadannan sune wadanda Allah ya yi fushi da
su.
(3) Wadanda suke aiki tukuru amma ba
tare da ilimiba, wadannan sune batattu.
Kammalawa: Daga takaitaccan
wannan jawabi ya bayyana agaremu ashe ibada ta ka su kashi-kashi, akwai ta
kabbai, akwai ta zuciya akwai kuma ta zahiri, kuma ita ibada hanyace da mutum
zai sami yarda Mahaliccinshi domin yanayin abinda Mahaliccin ya yarda dashi,
amma duk wannan zai same su ne idan mutum ya bi karantarwar farin jakada
Ma'aikin Allah Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi, kin yin aiki da
karantarwa yanasa Allah ya yi fushi da mutum, kamar kuma yin aiki ba akan
karantarwarba yana sa mutum ya kasance cikin batattu. Allah Ya tsaremu.
Aliyu Muhammad Sadisu,
Kwakungu, Minna, Jahar Neja Nijeriya.
Za'a iya tuntuba a (+234)08064022965,
ko kuma a: e-mail:aliyusadis@gmail.com
Ko a ziyarcemu a yanar gizo, a :
htt:// munbarin-musulunci.blogspot.com
mashaAllah jazakallah khair
ReplyDeleteMasha Allah! May Almighty Allah reward you abundantly
ReplyDelete