Shinfida: Bayan da bayanai
suka gabata akan abinda ya shafi karamin hadasi wanda yake ya takaitune ga
tsarki da kuma alwala, sannan bayanai suka zo akan abinda ya shafi kadan daga
cikin hukunce-hukuncen alwala, to a yanzu za'a yi bayani ne akan abinda ya
shafi babban hadasi wanda yake bai tsaya ga tsarki ko alwalaba a'a, shi
tsarkinsa shine ayi wanka shine an tsarkaka, wadannan abubuwa da suke wajabta
wanka suna da yawa za mu yi iya kokari damin mu kawo su daki-daki, da fatan
Allah ya yi mana jagora, amin.
(1) Janaba: Janaba dayace daga
cikin abubuwan da suke wajanta wanka, wanda yake hanyoyin kasantuwa da janaba
sune kamar haka:
(a) Fitar Mani: Idan maniyyi ya
fita daga mace ko namiji to wanka ya wajaba, amma kafin wankan ya wajaba sai ya
zama maniyyin ya fitane ta hanyar jin dadi, kamar kallo ko wasa ko tabe-tabe ko
jingina…' amma idan ya fita ba ta hanyar jin dadiba ya fitane ta hanyar wahala,
kamar ya taka wuta ko harbin kunama ko kuma watar lantarki ta ja shi…' to
wannan wanka bai wajaba a kanshiba saida kawai ya yi alwala. Shi wannan fitar
maniyyi da ake Magana akan shi ko dai ya fita a farke ko kuma ya fita ana
bacci, idan ya fita ana farke shine ake maganar an ji dadi ko ba'a ji ba, amma
idan ya fita ana baccine to ba wata maganar jin dadi wanka ya wajaba.
(b) Shigar Azzakari
Cikin Farji: Idan kan kaciyar namiji ya bace cikin gaban mace to wanka
ya wajaba. Anan ba'a maganar an fitar da mani ko ba'a fitarba, da zarar hakan
ya faru ko macen ce ta fitar amma namijin bai fitarba ko kuma namijin ne ya
fitar amma macen bada fitar ba ko ma dukansu basu fitarba wankadai ya kamasu su
duka, da wanda ya fitar da wanda bai fitarba, tunda ba maganar fitarwa ake yi
ba maganar saduwace, amma inda wasa aka yi ba saduwa ba to wanda ya fitar shi wanka
ya wajaba a kanshi.
Idan aka yi saduwa sannan aka kara yi to
idan an tashi wanka wanka guda kawai za'a yi, koda an yi saduwar sau gomane
sannan ake so ayi wanka to wanka guda za'a yi ba wanka goma ba.
Idan mutum ya sadu da mace kuma yake so ya
jinkirta wankan janaba zuwa an jima to abinda zai yi shine ya yi tsarki sai ya
yi alwala, domin alwalar tana rage kaifin janaba, sannan kuma tana kara kuzari
lokacin da ake so akara saduwar.
Idan mutum ya sadu da mace sai bai fitar da
maniyyi ba wanka ya wajaba akanshi kamar yadda bayini ya gabata, to bayan ya yi
wankan sai kuma ya ga maniyyi ya zubo, to anan idan wata sabuwar sha'awace ta
fitar da wannan maniyyin wani wankan ya kama shi, amma idan janabar da ya yi wa
wankace maniyyinta ya zo yanzu to alwala kawai zai yi.
Abayan da suka gabata mun yi bayani na
babbancin maniyyi da kuma maziyyi, sannan kuma da banbance-banbancen maniyyin
mace da na namiji. Sannan mu sani wadannan bayanai sun shafi maza da mata,
sannan kuma ka'ida ta musulunci itace bayanin abubuwa a yadda suke, domin kada
a ga maganganun sun yi tsauri, mahalline na bayanin hukunce-hukunce.
Fitar maniyyi a farke ko ta hanyar nafarki,
kamar mutum ya yi mafarkin yana saduwa da mace, ko mace ta yi mafarkin namiji
yana saduwa da ita to wannan al'amari yana tabbatar da abubuwa kamar haka; abu
na farko wannan wanda ya fitar da maniyyin janaba ta hau kanshi, abu na biyu;
idan wannan shine fitar maniyyinsa na farko to ya sani daga wannan lokacin ya
balaga, saboda haka hukunce-hukuncen musulunci sun hau kanshi ko kanta.
Idan mutum ya yi mafarkin yana saduwa da
mace, ko mace ta yi mafarkin ana saduwa da ita, sannan kuma ya farka bai ga
maniyyi ba to ba wata janaba akanshi, saboda haka ba zai wanka ba kuma zai yi
tsarkiba saboda hakan.
Wadannan kadan kenan daga cikin bayanan da
suka shafi janaba, kuma dole a tashi tsaye domin a karantar da mutane, wani da
ake Magana da shi cewa yake yi shi bai san idan mutum ya sadu da matarsa wai
sai ya yi wankaba, wai abinda ya dauka shine wanda ya yi zina shine wanda zai
yi wanka. Wannan jahilci har ina!.
Abubuwan Da Janaba
Ke Hanawa: Bai halatta ga wanda yake da janaba ba ya shiga masallaciba, ko kuma ya
karanta Alkur'ani ba, sai aya daya ko biyu domin neman tsari.
Mutumin da yasan ba zai iya taba rowan sanyi
ba to malamai sunce kada ya kusanci iyalinsa sai ya tanadi abinda zai dumama
rowan dashi, kamar hita, risho ko itace…'.
(2) Daukewar Jinin
Al'ada: Abu na biyu cikin abubuwan da suke wajabta wanka shine daukewar jinin
al'ada, kenan idan jinin al'adar mace ya dauke to abu na farko dake gabanta
shine wanka. Bayanai akan abinda ya shafi jinin al'ada da hukunce-hukuncensa da
alamar daukewarshi da izinin Allah za su zo nan gaba, mudai sani idan jinin
al'ada ya dauke to dole mace ta yi wanka, kuma zuwan jinin al'ada lamace dake
nuna wannan mai jinin ta balaga musamman ace shine zuwansa na farko a wurinta,
bayanai dai za su zo da izinin Allah.
(3) Daukewar Jinin
Biji: Wannan shine abu na uku daga cikin abubuwan da suke wajabta wanka,
watau daukewar jinni haihuwa, da zarar mace ta ga jinin haihuwa ya dauke mata
ko da ranar data haihune to wanka ya wajaba akanta domin ta fara sallah, ba
wanda yace sai mai jego ta yi kwanaki arba'in kafin ta kama sallah, shima bayai
akan jinin biji zai zo da izimin mai duka shine Allah, kawai mu sani anan
daukewar jinin haihuwa yana wajabta wanka.
(4) Mutuwa: Mutuwa tana
wajabta a yiwa wanda ya mutu wanka, shi kuma bayanai kan abinda ya shafi wankan
da yadda ake yinsa zai zo ne alokacin da za'a kawo bayanai kan jana'iza da
izinin Allah, kuma Allah ya kaimu lokacin, abinda ake so a fahimta anan shine
idan mutum ya mutu to dole ayi mishi wanka sai dai idan shahidine da ya rasu a
fagen fama.
(5) Musulunta: Wannan yana cikin
abinda malamai suka karawa juna sani, shin idan wanda ba musulmiba ya musulunta
wajibine sai ya yi wanka? Wasu sukace wajibine domin Ma'aikin Allah –Tsira da
amincin Allah su tabbata a gareshi- ya umarci wasu da suka musulunta da su yi
wanka, su kuma wadanda sukace ba wajibi bane wankan sunce ba'a ruwaito cewa
Ma'aikin Allah –Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi- ya umarci dukkan
wadanda suka musulunta da cewa kowa sai ya yi wanka ba.
Kammalawa: A yanzudai munsan abubuwan
da idan yada daga cikinsu ya faru to wanka ya wajaba, kuma mun sami takaitaccan
bayani akan abinda ya shafi janaba, kama daga hanyoyin da ake samunta, bayanan
da zasu zo nan gaba za su kun yadda wankan tsarki yake, wato wankan janaba da
kuma na daukewar jinin al'ada (haila) da bambance-bancen dake cikin su, Allah
ya kai mu lokacin da sauran kwana da kuma imani.
Aliyu Muhammad Sadisu,
Kwakungu, Minna Jahar Neja, Nijeriya.
Za'a iya tuntuba a (+234)08064022965,
ko kuma a: e-mail:aliyusadis@gmail.com
Ko a ziyarcemu a yanar gizo, a :
htt:// munbarin-musulunci.blogspot.com
Jazakallahu bi khairan
ReplyDeleteJazakallahu khairan
ReplyDeleteJazakallahu bikhairan kasira
ReplyDeleteThis comment has been removed by the author.
ReplyDeleteMiye hukuncin da mutumin da mace ta tabamai azzakarinsa har maniyyi ya fito da hannu ta tabamai
ReplyDeleteMiye hukuncin da mutumin da daya taba azzakarinsa hartaikai maniyyisa yakusa fitowa sai yatuno Allah yahana saidaina kuma ance in maniyyi zai kafasa fitar tsayawa mitum zai yabushe ya janyomai matsala in yayi ya mutum zayi kenan
ReplyDeleteMazi anamar Wanka
ReplyDeleteNidai nayi mafarki inabacci Amman banji dadin komiba name zanyi tsalki sai naga sanyi a wandona Malang mite hukunci
ReplyDeleteJazakallahu Khairan
ReplyDelete