Sunday, October 14, 2012

HUKUNCE-HUKUNCEN SALLAR IDI


Gabatarwa: Dasunan Allah Mai yawan rahama maiyawan jinkai, tsira da amincin Allah su tabbata ga fiyayyan halittar Allah Annabin tsira Annabi Muhammad, da Iyalan shi da Sahabban shi baki daya. Bayan haka a wannan karon za mu karkata akalar mu zuwa wani bangare da ya ke hararomu a 'yan kwanakin nan, wannanan bangaran kuwa shi ne na SALLAR IDI! Domin mu ga yadda musulunci ya tsara mana komai abinda ya rage kawai a garemu shi ne bi, komai angama, Allah tabbatar da duga-dugammu akan tafarkin Ma'aikin Allah.
Mecece Sallar Idi: ''Ita sallar idi sallace da ake gabatar da ita a wani lokaci kebantacce, awata siffa kebantacciya, sau biyu a shekara''. Kafin mu kai ga fashin bakin wannan ta'arifi na sallar idi, bari mu gabatar da tabbatuwarta tukunna.
Tabbatuwar Sallar Idi: Sallolin idi guda biyu da musulunci yake da su (Karamar Sallah da Babbar Sallah) kowacce ta tabbata a shara'a, ba wai bikine haka kwai na gargajiyaba.
Tabbatuwar Karamar Sallah: itace sallar da ake gabatarwa a ranar 1 ga Shawwal, don godiya ga Allah akan baiwar da ya yi mana na kammala azumin watan Ramadan, wannan sallar ta tabbata a Suratul-A'alah aya ta:14-15, Allah madaukakin sarki yana cewa: ''Tabbas duk wanda ya bayar da zakka (Fidda-kai) ya rabauta. Kuma ya anbaci sunan UbangijinSa sannan kuma ya yi sallah''. Sai malamai sukace 'Zakka da aka anbata a ayar farko itace zakkar fidda-kai, Sallah kuma da aka anbata a aya ta biyu itace, karamar sallah domin itace ake fitar da zakkar Fidda-kai kafin a ta fi, sannan kuma ga zikirin da aka an'anbata shine wanda ake yi lokacin tafiya sallar idin'.
Tabbatuwar Babbar Sallah: Ita kuma sallah ce da ake gabatar da ita a ranar 10 ga watan Zul-Hajji. Ita ma babbar Sallah ta tabbata a Suratul-Kauthar a aya ta: 2. a inda Allah madaukakin sarki yake cewa ''Ka yi Sallah domin Ubangijinka, kuma ka soke (abin hadayarka)'', malamai sukace 'Babbar Sallah ce domin an hada Sallah da Yanka' a ayar kamar wacce ta gabata an'hada Zakka da Sallah. Wannan tabbatuwar  wadannan sallolike nan ta ayoyin alkur'ani, hakanamma sun tabbata ta ayyukan Ma'aikin Allah –Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi-, Bukhari da Muslim da Abu-Daud da Nasa'i duk sun ruwaito daga Jabir-Allah Ya kara masa yarda yace ''Na harci Sallar idi tare da Ma'aikin Allah –Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi- sai ya fara gabatar da sallah kafin Huduba ba tare da an yi kiran sallaba ko an tada Ikama''. Haka shima Bara'u dan Azib –Allah Ya kara masa yarda yace ''Ma'aikin Allah –Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi- ya yi mana huduba a ranar babbar sallah, bayan ya idar da sallah sai yace ''Duk wanda ya yi wannan sallar tamu, kuma ya yi yanka irin namu to yankanshi ya yi daidai, wandako ya yanka kafin ayi sallah to wannan bashi (da ladan) yanka''. Wannan hadisin malaman Hadisi bakwaine suka ruwaito shi.
Hukuncin Sallar Idi: Hukuncin sallar idi shine, Sunnace mai karfin gaske, domin Ma'aikin Allah –Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi- ya aikata ta kuma ya lizimceta, hakanan kuma ya fitar da mata da kanan yara zuwa halartar wannan sallah. Saboda haka bai kamata mutum ya yi sakaci da itaba har ya rasa samun wannan sallah wanda saboda ita nema aka bada hutu a kasa baki daya, ka rufe shagonka na kasuwanci ka dakatar da ayyukanka.
Lokacin Sallar Idi: Kamar yadda bayani ya gabata a ta'arifi cewa sallace da ake gabatarwa a lokaci kebantacce to wannan lokacin kuwa shine ''Daga lokacin da rana ta fito ta daga kamar tsawon sandar mashi harzuwa lokacin da rana zata karkata daga tsakiyar sama''. Amma malamai sukace 'An fi so a babbar sallah a yi ta da wurwuri domin mutane su samu su koma gida domin su yanka layyarsu a daidai lokacin walaha, sannan kuma su ci abinci domin basu ci ba suka fito sallah. Amma akaramar sallah an fi so a dan jinkirta sallar domin mutane su samu su gama fitar da Zakkar su ta fidda-kai, su kuma ci abinci domin iti an fi so a ci kafin a fito sallah'.
Ladubban Sallar Idi: Akwai wadansu ladubba da yakamata a ladabtu da su, wadannan ladubba suna da yawa daga ciki akwai:
1.       Yin wanka da sanya turare da kuma sanya tufafi masu kyau sababbine ko nada.
2.       Hakanan yana daga cikin labudda a ci abinci kafin a fita sallar idi a karamar sallah, da kuma jinkirta cin abinci a babbar sallah har sai an yi sallah, da kuma cin wani abu na hantar dabbar layyah ga wanda ya yi. Ankarbo daga Buraidah –Allah Ya yarda da shi- yace; ''Ma'aikin Allah –Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi- ya kasance baya fita zuwa masallcin idi a karamar sallah har sai ya ci abinci, kuma ya kasance baya cin abinci a babbar sallah har sai ya dawo daga masallacin idi, sai ya ci wani abu na dabbar layyarsa''.wannan Hadisi Tirmizine ya ruwaito.
3.        Kana yana daga cikin ladubba yin kabarbari, kuma lafazinta shine: Allahu Akbar, Allahu Akbar, La'ilaha Illallahu, Allahu Akbar, Allahu Akbar, Walillahil Hamd.
4.       Yin gaisuwar sallah wato kacewa dan'uwanka musulmi ''Allah Ya karba mana ya karba muku''.
Siffar Sallar Idi: Kamar yadda ya gabata a farkon bayani cewa sallace da ake gabatar da ita a wata siffa kebantatta, wannan siffa kuwa itace; wannan sallah ana yin ta ne Raka'a biyu, kuma ana bayyana karatun, ba tare da angabatar da kiran sallah ba, ko tada ikama, sannan kuma ba'a gabatar da nafila kafin sallar ko bayan sallar. A raka'ar farko bayan kabbarar harama anayin kabarbari shida kafin fara karatu (wato kabarbari bakwai kenana). A Raka'a ta biyu bayan kabbarar tasowa sai a yi kabarbari biyar, kafin fara karatu (wato kabarbari shida kenan), wadannan kabarbari liman da mamu duk suna yinsu sai dai mamu baya karatun sallah saboda karatun liman, sannan sai ayi sallar kamar sauran salloli, bayan liman ya yi Tahiya ya yi sallama sai ya gabatar da Huduba, sannan yana da matukar muhimmanci a tsaya a saurari hudubar, wadannanfa sune ayyukan ranar, amma wacce gaggawa mutane suke yi suke barin sauraron Hudubar?.
Wanda bai samu sallar idi ba ya samu ya yi sallah Raka'a hudu kamar nafilfili, idan kuma ya ga dama ya yi ta a siffar sallar idi.
Idan kazo ka sami liman yana Tahiya sai ka zauna tare da shi, idan ya yi sallama sai ka mike ka kawo raka'oinka biyu a siffar su da ta gabata.
Wadansu Mas'aloli: A yanzu za'a kawo wadansu halaye da mutum yakan samu kanshi a ciki idan ya zo ya samu tuni anfara sallah.
1.      Idan mutum ya zo ya sami liman ya kammala kabarbari ya fara karatu ya zai yi?. Amsa: Anan zaka yi wadannan kabarbarin, kasancewar ba abune mejan lokaci ba, sannan sai ka raurari karatun liman.
2.       Idan ka zo ka sami liman ya fara kabarbari amma bai gamaba, to anan zaka yi sauran kabarbarin da suka ragewa liman tare da shi, sannan sai ka kawo wadanda suka wuceka, koda liman ya fara karatu, kenan anan ba zaka yi wadanda suka wucekaba a lokacin kabarbarin liman.
3.      Idan kazo ka sami liman yana Ruku'u sai ka yi kabbarar harama kadai ka bishi, ba sai ka kawo sauran kabarbarinba.
Tambihi: Ya kamata mu san girman wadannan salloli da matsayinsu a addini, tunda har yakai Ma'aikin Allah –Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi- yana cewa a fita sallar har da mata da kananan yara, har mata marasa tsarki idan sun je sai su yi nesa da wurin sallah idan anzo huduba suma sai su anfana. Kada mu sha'afa akan wannan sallarne aka bada hutu duka kasa, aka rufe shaguna kada mutum ya shagala a wannan lokaci da abinda zai hana mishi samun wannan sallah. Sannan kuma a kula da yara da irin suturar da za su sa, domin idan ka ga wadansu yaran ba kace 'ya'yan musulmi bane, wannan baidace ba kuma baikamata, wasu kuma rawa kamar mazari, Allah Ya sawwaka, amin.
Kammalawa: Daga wadannan bayanai da suka gabata ya bayyana a garemu cewar sallar idi ba wata gargajiya bace ibadace da Allah ya shar'anta ta ta harshen fiyayyan halitta Annabi Muhammad –Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi-, itako ibada anayinta akan yadda aka tsarata ne, Allah ya karbi ibadarmu ya sa ayi sallah lamilafiya ya tsaremu ya tsare mana imaninnu, amin.
Aliyu Muhammad Sadisu,
 Kwakungu, bayan Ofishin 'Yansanda,
Minna jahar  Neja Nijeriya.
 Za'a iya tuntuba a.
G.S.M. (+234)8064022965.
 e- Imei : aliyusadis@gmail.com
htt:// munbarin-musulunci.blogspot.com
www.fecebook.com/Aliyu Muhammad Sadisu
www.youtube.com/Aliyu Muhammad Sadisu

Wednesday, October 3, 2012

Aikin Hajji A Wannan Shekarar 1433 (2012) Ina Mafita??


Da sunan Allah mai yawan rahama mai yawan jinkai, tsira da amincin Allah su tabbata ga ma'aikin Allah. Bayan haka lalle wannan masifa da ta aukawa kasarnan a wannan gagarumin aiki wanda yake rukunine daga cikin rukunan addinin musulunci abin a tsaya ai nazarinta ne domin aga ta ina ta fito kuma ya za'a tunkareta ta yadda ba zata sake aukuwaba, domin ace mutum ya isa kasa mai tsarki lamilafiya amma kuma a dawo da shi kai wannan ba karamin tashin hankali bane Ya Allah muna rokonka da kada musake ganin maimaituwar wannan al'amari. Kamar yadda na fada lalle ya kamata mu tsaya mu yi wa wannan lamari karatun ta-natsu, mabudin wannan karatu itace ayar dake cikin Suratus Shura aya ta 30. ''Kuma duk abinda ya sameku na kowacce irin masifa to fa saboda abinda kuka gabatarne, kuma (Allah) Yana ga abubuwa masu tarin yawa''.
          Lalle la'akari da wannan ayar yana dakyau mu tsaya muga me aka gabatar da ya haifar da wannan al'amari don asan matakin da za'a dauka don hana aukuwar irinshi nan gaba. Ni a ganina wadannan al'amurra sune kamar haka:
1. Mahrami: Shine mutumin da yake haramunne ya auri matar da yake tare da ita (kamar uba mahramine na 'yarshi, ko kaka ko siriki) shi yasa sai ace mahrami ko miji, Ma'aikin Allah –tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi- yana cewa: Bai halatta ga dukkan matar da tai imani da Allah da ranar lahira da ta yi tafiya kwana guda ba tare da maharraminta ba'' Hadisai da suka zo daga ma'aikin Allah –tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi- a kan haka suna da matukar yawa da fayyace al'amurra a fili da suke nuna irin gatan da musulunci ya yi mace lura da cewa ita mai raunice baibukar taimakoce a koda yaushe  kuma ko wanne iri. An ruwaito cewa wani daga cikin Sahabban ma'aikin Allah –tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi- an sanyashi cikin wadanda za su tafi yaki sai yace medakinshi zata tafi aikin hajji sai ma'aikin Allah –tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi- yace acire sunansa ya tafi ya je ya yi aikin hajji tare da maidakinshi. Kuma wannan al'amarii sannannene cewa alokacin da mace take tare da mahraminta ko mijinta zata dada kamewa doruwa akan wacce take da ita, in kuma ba kamammiya bace to zata kame da izinin Allah, kuma zata zama tana da abokin hira a wannan tafiyar, hikimomi da zaka iya zakulowa cikin muhimmacin mahrami a tare da mace a Halin tafiya ba karamin al'amari bane, duk wanda ya taba yin aikin Hajji zai tabbatar da muhimmancin mahrami tare da mace, ba Mijin-Biza ba domin akwai halin da ake shiga na sai ka rike mata hannu ko jiki, wanda yake haka ba zai yiwuba idan ba maharramaka bace. Malamai sun karawa juna sani kan abinda ya shafi aikin Hajji shin idan aka sami tawaga amintacciya  mace zata iya tafiya a cikinsu ko dab a mahraminta? Sai wannan tawaga ta zama kamar mataimaka a gareta? Malamai da yawa sun tafi akan haka,
          Maganar mahrami maganace da ta taso a aikin Hajjin wannan shekarar ta 1433 Hijira ko 2012 miladiyya, a inda akan hakanne hukumar kasar Saudiya ta dawo da mahajjata mata masu tarin yawa daga kasar, na farko da maganar mahrami tabbatacciiyace a shara'a domin ta fitone daga bakin Ma'aikin Allah –tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi- ba Magana bace da hukumar kasar Saudiya ta kirkiri bam domin na ji Nura Das Ahirarsa da jaridar Leadership Hausa bugu na 313, a shafi na 25 yana cewa Ba kowanne mahajjaci bane ke bin akidar Wahabiyaci, Su a mazahabinsu na Ja'afariyyah wanda aka fi sani Shi'a mace idan ta amincewa kanta ko waliyyanta sun amince mata zata iya tafiya ko inane, wannan Magana tasu ta nuna abinda acewa su Shi'a ba abinda ya hada su da karantarwar ma'aikin Allah, in banda ina maganar bin tafarkin ma'aikin Allah ina kuma maganar wahabiyanci?. Maganar maharami manace data mamaye kafafan yada rabaru a kasarnan kuma maganace da take bukatar a tsaya a yi mata karatun-ta-tsau domin sanin hikimomi da tausayawa da musulunci ya yiwa 'ya mace, kafafan yada labaru sun cancanci yabo yadda suka tunubi malumma akan wannan al'amari wato suka maida al'amarin zuwa ga masu shi. To amma hanzari-ba-gudu-ba maganar da kafofin yada labarai suke yi na cewa anya maganar mahramce kadai tasa wannan al'amari ya faru koko akwai lauje cikin nadi domin mata 'yan Nijeriya kawai aka dawo da su banda 'yan wadansu kasashen? Wannan maganar ya kamata a yi la'akari da ita, wannan ya kaimu abu na biiyu wato.
2. Gurbacewar Tarbiya: A gaskiya Najeriya tana da matukar kima da daraja a idanun kasar Saudiya, amma a gaskiya halayyar da 'yan Najeriya suke nunawa a wadannan wurare masu tsarki musamman ma a birnin Makkah birni mafi tsarki da daraja gaskiya a kwai bantakaici, mata nawane suka tsallake mazajensu su kai zaman dirshan a birnin makkah, me ya kaita? me take yi? Asalin Magana a musulunci mace bata ciyar da kanta kwata-kwata, idan ta yi aure mijinta ya ciyar da ita idan batai aure ba mahaifinta ko waliyyinta ya ciyar da ita. Duk mutumin da ya tabayin aikin hajji zai ga irin halayya da sutura ta rashin mutunci da wasu matan -wasu cikin mahajjata- suke nunawa a ranar sallah matsattsun kaya wasanni marasa kyau tun kafin a gama zaman mina, ballantana a gidan da alhazai suka sauka ka ga yadda ake da 'yan-tuwo-tuwodin abin zai baka mamaki kamar ba a kasa mai tsarki ake ba, idan akai maganar dogon-gida ko Sara-Mansur abirni Makkah da sauran unguwanni kamar su Jabal abin ba'a cewa komai. Ni inagani ya kamata ofishi Najeriya ya shirya wata bita da karantar da 'yan Najeriya da tarbiyantar da su a biranan Makkah da Jiddah da kuma Madina, kuma ya tashi tsaye yaga 'yan Najeriya suna zaune akasar a bisa doka, anan ba ina cewa duka 'yan Najeriya haka suke ba a'a kwata-kwata, akwai tsayayyu, amma mu sani idan fitina ta zo ba tana takaituwa bane ga wadanda suka janyota kamar yadda muka gani a wannan shekarar, zaka iya samun macan da bata ganin jirgin sama a kasaba sai wannan karon amma gashi bala'in wasu ya janyo mata, Allah Madaukakin sarki yana cewa:
          ''Kuma ku ji tsoron fitina wacce ba ta samun danda suka yi zalunci daga cikinku kadai, kuma ku sani lalle ne Allah Mai tsanani ukuba ne'' Sutul-Anfalm aya ta 25.
Mai karatu idan kana jin abinda 'yan Najeriya suke aikata a kasa mai tsarki musamman mata abin zai dauure maka kai matuka da gaske, yanzu idan aka ce maka dukkan matan da suka je Umarar nan data wuce sun dawo nan Najeriya? Me zakace ko kuma ka tambaya.
          Sannan suma hukumar alhazai ta Najeriya ya kamata ta tashi haikan wurin sanyawa maniyyata tsoron Allah da kula da dokokin Sa, a samu malamai masu tsoron Allah wadanda ba himmarsu a biya musu kujeraba, wadannan dakakkun malamai sukasance na dindin-din ko kaso mai yawa daga cikin su sannan abasu damar gudanar da aikin nasu.
3. Mace mai Juna-biyu: Lallekan akwai maganar wahala ga mace mai juna-biyu a aikin hajji mutum ma yana shi kadai ya yacika, amma irin matakin da hukuma ta dauka na haramtawa mace mai juna-biyu aikin hajji wai koda kuwa na wata dayane gaskiya ya kamata a sake duba wannan Magana idan andubeta ta bangaren kiwon lafiya a dubeta ta bangaren addini, babu wani dalili aduk abinda malamai sukai ijima'i aka kafa dalili da shi da ya nuna cewa mace mai juna-biyu bata da damar zuwa aikin hajji, ni ina jin tsoro kada irin wannan hani da aka yiwa wadannan matan yasa aka wannan dayyar matsalar, kada mu sha'afa maganar addini ake yi asalima shi aikin hajjin ginshikine daga cikin shika-shikan musulunci guda biyar, saboda haka kada ka kuskura ka hana wani wannan aiki ba tare da kanada kakkarfan dalili da zaka gabatarwa Allah ba a ranar kiyama, a shekarar da Ma'aikin Allah –Tsira da amincin Allah su kara tabbata a gareshi- Ya yi aikin Hajji wanda shine kuma akekira da hajjin bankwana, adaidai lokacin da Ma'aikin Allah ya isa Zul-Hulaifah inda nan ne mikatin mutanan madina yana zuwa wurin medakin Sayyidina Abubakar ta sauka (tahaihu), kaga kenan ta fito ne ma da tsohon ciki, awannan tafiya da ake akasa ko a doki ko a rakumi, wanda ba za'a hada hakan da jirgin-sama ba ko na ruwa ko mota ba. Wannan matsananciyar dokar data zamar da mata da yawa Hajji Haram ya kamata a sake dubata, wadda ta sanadiyyar ta ake ruwaito mata da yawa suna zubar da cikinsu, irin wannan mataki na anfani da na'urori masu gani harhanji masu ganin-kwakwaf na cewar indai har anbankado cewar tana da ciki to Hajji Haram ya kamata a sake dubawa.
Shawarwari/Mafita: Ni ina ganin bin wadannan shawarwari zai zama wata mafita ga rashin sake maimaituwar irin wannan al'amari, da muke rokon Allah Ya kiyayemu daga maimaituwar wannan alamari:
1.     Tsayawa da tabbatar da mahrami shar'antacce muddin akwai yadda za'a same shi  ba abinda ake cewa mijin-biza ba.
2.     Gabatar da cikakkiyar bita akan mece ''Rifka Ma'amuna'' sannan suwaye, a kuma gabatar musu da bita ta sanin makamar aikin ''Rifka Ma'amuna''.
3.     Tashi tsaye domin a wayar da kan mutane dangane da matsayin mahrami a shara'a, da kuma bayanin gatan da musulunci ya yiwa mata akan sanya musu mahrami da ya yi.
4.     Kimsawa maniyyata tsoron Allah madaukakin sarki, da kuma falalar da maibin Allah yake da ita da kuma narkon sabawa Allah, a gida Najeriya ko a kasa mai tsarki.
5.     Kimsawa maniyyata bin tafarkin Ma'aikin Allah da kuma cewar rabauta duniya da lahira ta tattarune akan tsantsanta biyayya ga reshi.
6.     Karfa halartar maniyyata  wuraran bita.
7.     Samar da wata manhaja ta baidaya kakkarfa akan abinda ya sha fi bita.
8.     Kara samarwa malamai masu tsoron Allah gurabu a harkar hajji, da kuma basu karfin fada aji.
9.     Kara sa ido da dokar da ta dace ga duk wanda ya yi fitsara a duk wurin da ya shafi Hajji tun daga wuraren bita har kamala aikin hajji.
10. Sanya ido ga dukkanin jahar da ta bari wani alhajinta ya ki dawowa.
11. Karamin ofishin jakadancin Najeriya dake birinin Jiddah ya samara da wata ganawa da 'yan Najeriya dake Makkah, Jiddah da Madina domin karantar da su da kuma kara nuna musu tsarkin wurin da suke zaune.
12. Daukar matakin ladabtarwa ga duk dan Najeriyar da ya karya ittifakiyar da aka yi da kasar Saudiyyah.
13. Sake duba maganar mace me juna-biyu, domin kada mu manta tun kafin Saudiya su nemi su zamar da wasu mata Hajji Haram tuni Najeriya ta zamar da wasu.

          Allah madaukakin sarki ya tsaremu ya tsare mana imanimmu, ya kawo mana karshen wannan kiki-kaka da ake yi da alheri, Allah ya kai alhazammu mata da maza kasa mai tsarki lafiya ya kuma dawo mana da su lafiya. Ya Allah katsare mana kasarmu ka zaunar da mu lafiya da dukkanin kasashen musulmi bakiya, amin.
Aliyu Muhammad Sadisu,
 Kwakungu, bayan Ofishin 'Yansanda,
Minna jahar  Neja Nijeriya.
 Za'a iya tuntuba a.
G.S.M. (+234)8064022965.
 e- Imei : aliyusadis@gmail.com
htt:// munbarin-musulunci.blogspot.com
www.fecebook.com/Aliyu Muhammad Sadisu
www.youtube.com/Aliyu Muhammad Sadisu

KURAKURAI A KIRAN SALLAH


بِسْمِ اَللهِ اَلرَّحْمَنِ اَلرَّحِيمِ
Gabatarwa:
Dasunan Allah maiyawan rahama maiyawan jinkai, tsira da amincin Allah su kara tabbata ga fiyayyan halittar Allah, manzan tsira Annabi Muhammad da Iyalan Sa da Sahabban Sa baki daya da wadanda suka bi bayansu da kyautatawa izuwa ranar sakamako, amin.
Bayan haka, hakika wannan bita da 'yan uwa suka shirya a Shirin Hasken-Musulunci anan Minna, fadar Jahar Neja ayau (Alhamis: 4, ga Ramadan 1432 daidai da 4, Agusta 2011) lallai tana da matukar muhimmanci musamman a irin wannan lokaci, wanda yake a fili take irin gudun mawar da ladanai suke bayarwa a cikin al'umma baki daya.
          Wannan matashiya da zamu tattauna a kanta maitaken "Kura-Kuran da ake samu a kiran sallah'' muna fatan ta zama wani abune da za mu yiwa juna gyara, don gyara kayanka bai zama sauke mu raba ba, kuma muna so a wannan haduwa ya zana an magance wadannan kura-kurai duddacewa ba su ke nanba, amma har idan muka gane cewa akwai kurakuran kuma muka dauki hanyoyin gyara to zamu sami taimakon Allah akai, Allah ya yi mana jagora amin.
          A cikin wadannan kurakurai akwai wadanda su ke da alaka da maikiran sallah, akwai kuma wadanda suke da alaka da ma'anonin kiran sallah ta yadda idan ma'anar ta canza sai ta maida shi ba kuma kiran sallah ba. Sannan akwai wadanda suke da alaka da al'umma baki daya, lalle wanan yana nuna mana cewa matsayin ladaini a cikin al'umma ba karamin matsayi bane, muna rokon Allah da sunayan kyawawa da siffofin sa madaukaka ya yima jagora amin.
          A yanzu za'a dan lissafa wasu daga ciki, ayi kuma dan karin haske sannan abada shawarwari.
Akwai wadansu abubuwa da zasu shiga cikin kura kuran da ake samu a kiran sallah, kamar:
1. Rashin Kiran Sallah A Farkon Lokacinta: Kamar yadda malamai suka zayyana bayana a littafai cewar kiran sallah shi ne: Sanar da mutane shigar lokacin sallah. Kuma kamar aka sani kowacce sallah tanada lokacinta kuma gashi malam ya kara mana bayi ya kuma fito mana da lokatan fili, wanda rashin kiran sallah a farkon lokacin ta ya haifar da angama kiran sallah sai a tada ikama, wanda anasone tsakanin kiran sallah da tada ikama a sami tazara ta yadda mara alwala zai yi alwala, wanda sai ya yi tsarki ya je ya yi tsarki, anan kenan zamu gane yana daga cikin manyan ayyukan ladan da lokacin sallah ya yi ya kita domin ya sanar da al'umma shigar lokacinta.
          Babbancin kiran sallah da ikama shine: Kiran sallah sanar da mutane shigar lokacin sallah (Ladani kuma shi ya kamata ya fi kowa tantance lokutan sallah), ita kuma ikama: sanar da wadanda ke cikin masallaci anfara sallah.
2. Rashin Tantance Lokaci: Ladani ya sani shi ne mutum na farko da yafi kowa sanin canjin lokaci da yadda yake karuwa da kuma yadda yake raguwa, kuma idan zai yi anfani da agogo kada ya dogara da agogo daya, ya zamana yana dasu uku ko hudu, rashin wannan wadansu ladanan suke kiran sallah tsakaddare ko dab da magariba idan hadari ya rufe rana.
          Ladanifa ya sani sallolin mutane da azuminsu suna ratayene  a wuyanshi, miliyoyin mutane basa shanruwa ko su dakatar da sahur sai ladan ya kira sallah.
3. Rashin Tsayawa A Koyi Kiran Sallah: wannan yana daga cikin manyan matsalolin da ake samu, ta yadda inda za'a kowa ya fadi malamin da ya koya masa kiran sallah to da anyi zuffa. Hakan ya haifar da kowa yake yin yadda ya ga dama, wasuma ka ji da yarukansu suke yi ba da larabciba.
4. Rashin Tantacce Ladanai A Masallaci: wannan yasa kowa ya zama ladani, wanda yake wannan kuwa kuskure ne, wannan baihana a sami ladanai a masallaci gudaba, su zama biyu ko uku ko dai gwargwadon abida ya sawwaka amma tsayyayu, wannan zai sa asan cewa ladani wane yana kiran sallar asubahine kafin alfijiri ya keto amma ladani wane sai bayan alfijiri, kamar yadda ya kasance tsakanin Bilal da Ibnu ummi maktum Allah ya kara musu yarda.
5. Rashin Sanin Ma'anonin Kiran Sallah: wannan ya haifar da abubuwa masu yawa, da basa cikin addini, misali: Ladani ya kammala kiran sallah sai yace 'Ayi alwala, a jaddada' inda yasan ma'anar
حَيَّ عَلَى اَلصَّلاَةِ، حَيَّ عَلَى اَلْفَلاَحِ
Hayya alas Swalah, Hayya alal Falah da bai fadi waccar maganarba.
6. Rashin Kula Da Ladubban Sallah: wannan ya sa sai kaka ladani yana kiran sallah amma sai kaga kamar yana wani abu da bashi da alaka da addini, wani lokacin sai ya yi kamar ya juyawa alkibla baya.
7. Kura kurai a lafuzza: ana samun kurakurai masu tarin yawa a lafuzzan kiran sallah. Wadannan kurakurai sun kashi kashi biyu.
(a) Kuskure mai canza ma'ana: irin wadannan kura-kurai suna fitar da shi daga kiran sallah kwatakwata ya zama wani abu daban, misali:
اَللهُ أَكْبَرُ – أَكْبَارُ
(b) Kuskure na bata lafuzza: wanda yake fitar da shi daga duniyar larabci, misali:
أشْهَدُ أَنَّ مُحَمَّدًا رسولُ اللهِ
Shawarwari:
A takaitaccen wanna jawabi da kuma wadannan abubuwa dana gani ina bada shwara kamar haka:
1. Bayar da mintina bayan kiran sallah kafin tayar da sallah, wannan ko zai tabbatane idan ankira kowacce sallah a farkon lokacin. Misali Azahar minti 20 la'asar minti 15 magariba minti 10 lisha minti 15 asuba minti 20.
2. Ladani ya zama yana da agogo kamar uku banda na wayarshi, kuma ba zaije kiran sallah ba sai ya duba su duka.
3. Aiki da dukkan abubuwan da aka gabatar a wannan bita.
4. Gyara inda duk mutum ya ji yana da kuskure.
5. Isar da wadannan bayanai ga wadanda basu zo wannan bita ba.
6. Ladanai su samara da wata haduwa da zasu dinga yi lokaci lokaci domin tuntubar juna koda ko za'a fara a matakin unguwa unguwa ne.
7. Ci gaba da shirya irin wannan bitar lokaci bayan lokaci
8. Koyon kiran sallah baki da baki daga wurin malamai masana.
          Allah ya gafartamana ya kuma ya fe mana, Allah ya karbi ayyukammu amin summa amin.
وصلى الله وسلم على نبينا محمد وعلى آله وصحبه وسلم
Aliyu Muhammad Sadisu,
 Kwakungu, bayan Ofishin 'Yansanda,
Minna jahar  Neja Nijeriya.
 Za'a iya tuntuba a.
G.S.M. (+234)8064022965.
 e- Imei : aliyusadis@gmail.com
htt:// munbarin-musulunci.blogspot.com
www.fecebook.com/Aliyu Muhammad Sadisu
www.youtube.com/Aliyu Muhammad Sadisu