Wednesday, March 12, 2014

025- SUNNONIN SALLAH


Shinfida: Su sunnonin sallah su ne ke biye da farillan sallah wurin matsayi a cikin sallah, saboda haka kamar yadda bai kamata ka yi wasa da farillan sallah ba to haka yake bai kamata ka yi wasa da sunnonin sallah ba. Wasu da zarar sun ji ance abu kaza sunna ne to basa daukan shi da girma domin suna ganin rashin sa ba zai hana musu sallah ba, alhali kuwa wannan kuskurene mai girman gaske, ai ko ba’a sallah ba duk abinda ka ji an ce sunnane to bai kamata ka yi wasa da shiba.
   Su wadannan sunnoni na sallah kamar yadda bayani ya gabata matsayinsu baikai na farilla ba domin idan ka bar farilla daya a raka’a sai dai ka ajiye wannan raka’ar ka kawo wata makwafinta kamar yadda bayanai za su zo da izinin Allah a lokacin bayani kan kabaliyyah da ba’adiyya. Kennan su sunnonin sallah ba haka bane, idan mutum ya cika su to sallar shit a cika, idan ko bai cika su ba to sallar shi bata cika ba ko da ko ba zai sake ta ba. Saidai su sunnonin sallah asune ake samun damar kyaran sallah ta hanyar yin kabaliyyah ko ba’adiyyah, amma ita farilla ba’a yi mata hakan.
Sunnonin Sallah: su sunnonin sallah suna da yawa, sun fi farillan sallah yawa, ga kadan daga cikin su:
1.Tada Ikamar Sallah: Ita ikamar sallah ta shafi mai sallah shi kadai ko wadanda za su yi ta cikin jam’i, kuma bayananta sun gabata a Babi Na shabakwai (017).
2. Karatun Sura Bayan Fatiha: Kasancewar shi karatun Fatiha yana cikin farillan sallah to yanzu shi karatun sura bayan fatiha yana cikin sunnonin sallah ne, kuma wadannan bayanai sun shafi maza da matane baki daya, domin duk abinda aka umarci maza da shi an umarci mata das hi saidai abinda shar’a ta ware tace banda mata. Kuma mutum ya tashi ya koyi karatun sallah daga bakin malamai. Sannan mu sani shi karatun sura bayan fatiha ana yin shi ne a raka’o’i biyun farko, kenan banda na karshe, kamar haka: Asuba ana yi a duka raka’o’in, Azahar ana yi ne a raka’o’I biyun farko banda biyun karshe, la’asar ma haka, haka namma magariba banda dayar karshe, sannan ita ma isha banda biyun karshe.
3. Tsayuwa Domin Karatun Sura: Kenan kamar yadda karatun surar yake sunnane to hakama yin karatun a tsaye, kenan ba’a karatun sura a zaune sai dai idan akwai larura da shari’a ta yadda da ita.
4. Sirrantawa A Inda Ake Sirrantawar: Abinda ake nufi da sirrantawa shine ka motsa harshe domin yana furta karatun Alkur’ani, wato bakinka na motsi kenan, amma idan mutum ya yi shiru yai dunkum ba’a kiran wannan asurtawa. Inda ake surrantawa kuma sune: Azahar da la’asar bakidaya raka’oinsu, sai kuma raka’ar karshe ta magariba da kuma raka’oi biyun karshen Lisha. Haka kuma nafilfilin rana suma ana asurta su ne.
5. Bayyanawa A Inda Ake Bayyanawa: Idan kuma akace bayyanawa ana nufin ka jiyar da kanka da kuma wanda yake kusa da kai, wannan idan kai kadai kake sallah kennan, amma idan kai limanne to zaka daga murya yadda kowa zai ji, ai domin karatun limanne aka hana mamu su yi na su karatun.
   Kuskuren da ake samu anan shine, idan mutum ya shigo masallaci zai yi sallah ko kuma ya mike yana ramo raka’o’in da suka wuce shi sai ya bude baki yana karatun sallah da karfi, wanda wannan yana shiga cikin karatun wani, yana kuma hargitsawa wani nashi karatun, inda kowa zaibi yadda bayan suke to da an yi komai cikin jin dadi da walwala, zuwa inda ake karatu shi zai magance wadannan matsalolin.
   Wuraran da ake bayyana karatun sallah kuma sune kamar haka; Karatun sallar asuba baki-dayanta, raka’ar karshe ta sallar magariba, da kuma raka’o’in karshe na sallar lisha.
6. Kabarbari: Dukkanin kabarbarin sallah sunnane in banda kabbarar farko wacce take ita farillace wato kabbarar harama. Saidai malamai sun karawa juna sani akan cewa; shin dukkanin kabarbarin a dunkule suke sunnan guda koko kowacce kabbara sunnace mai zaman kanta?.
7. Tahiyyah: Itama tana cikin abinda ya kamata mutum ya koya daga bakin malami kai tsaye, yana karantawa kana karantawa, domin ana samun kura kurai masu tarin yawa a lokacin mutane suke karantata.
8. Zama Domin Tahiyyah: Ashe itama ba’a yinta a tsaye, kuma inda mutum zai zauna amma bai karantata ba to yabar sunnah guda daya, idan kuma ya manta bai yi zaman farkoba misali to yabar sunnoni biyu kenan, karatun tahiyyar da kuma zama domin karatunta.
9. Gabatar Da Fatiha Kafin Surah: Inda mutum zai zai fara karanta surah sannan ya zo ya karanta fatiha to da ya bata tsarin sallah, domin yadda ake so shine ka fara gabatar da fatiha sannan ka sai ka karanta surah.
10. Bayyanar Da Sallama: Kenan ita sallama ba’a asurce ake yenta ba, ana bayyana tane, anan mu ban-bance shi yin sallamar wajibine, amma yenta kuma a bayyane sunnane daga cikin sunnonin sallah.
11. Salati Ga Ma’aikin Allah: Yin salati ga manzon Allah –tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi- yana daga cikin sunnonin sallah. Kuma shi salati ga ma’aikin Allah yana da muhimmanci da lada da kuma falala mai zaman kanta, malamai sun kawo sigogi na salati ga ma’aikin Allah a kicin littafansu kamar mai littafin Ashmawi ya kawo haka nan ma mai littafin Iziyyah da kuma mai Risalah, mafi kyawun littafi da aka rubuta domin bayanin salati ga ma’aikin Allah shi kadai, shine littafin ‘Jila’ul Afham’, zaka same a shagunan da ake sayar da littafan musulunci.
12. Suturah: Duk wanda yake sallah shi kadai ko shine liman to anan ana bukatar ya sanya suturah a gabanshi, domin baiwa mai wucewa damar wucewa ta bayan suturar, amma shi mamu baya sanya sutura domin suturar liman ta wadatar masa, saboda haka idan kuna sallah da liman sai wani ya wuce ta gabanku babu komai inda ba ya wuce ta tsakanin liman da suturarshi bane.
  Kammalawa: Adaidai nan zamu da katata, dafatan wadannan takaitattun bayanai sun wadatar, sannan kuma zamu ci gaba da kara kusantar malumma. Kula da wadannan ayyuka a cikin sallah bakaramin aiki bane, domin shi ke sa mutum ya samin dandano na zakin sallah, domin ya bata kulawa ta hanyar lura da farillanta da kuma sunnoninta, dudda cewa anan kadan muka kawo, a karo na gaba zamu kawo bayanaine akan Mustahabban Sallah, sai Allah ya kai mu.
Aliyu Muhammad Sadisu,
 Minna Jahar  Neja, Nijeriya.
 Za'a iya tuntuba a (+234)08064022965,
ko kuma a: e-mail:aliyusadis@gmail.com
Ko a ziyarcemu a yanar gizo, a :
htt:// munbarin-musulunci.blogspot.com
   

5 comments:

  1. Jazakallahu khairan.Malam ina kara mika kokon baran Neman Karin sanin sauran Sunnonin Sallah.ko da kuwa a kasida ta gaba a sanyo mana sauran iya Gwargwado.Allah shi taimaka ya Kuma sa muyi tarrayya alada amin Thumma amin.

    ReplyDelete
  2. Gaskiya naji dadin wannan bayanin, Allah yasa mudace

    ReplyDelete
  3. Allah ya saka wa Malam da mafificin Alkhaeri. Ya kuma sa mu gama da duniya lfy. Akramakallah mun ji dadin kasancewa da wannan karatun. Allah ya saka da gdn Aljannah

    ReplyDelete