Shinfida: Lalle wannan babi
yana da matukar muhimmanci, domin bayan da kasan alwala to ya kamata kasan abin
da ke warwareta, akan haka ya ka yiwa kanka hukunci idan zaka yi sallah ko
abinda dole sai da alwala ake yinsa, saboda haka yana da matukar kyau mu kula
da wadannan hukunce-hukunce. Allah ya yi mana jagora.
Abubuwan da suke bata alwala sunkasu kashi
biyu; Hadasi da Sababinsa. Abin nufi anan shine, akwai abinda shi karankan sa
yake bata alwala to wannan shi ake kira Hadasi (Al'ahdaas). Akwai kuma
wanda shi karankan sa bai warware alwala amma zai kai ka ga abinda yake warware
alwalar to wannan shi ake kira, Sabuban Hadasi (Asbabul Ahdas).
To shi hadasin wato abinda yake karya alwala
da karankansa, abubuwane guda shidane, hudu daga cikinsu suna fitane ta gaba,
sune kuma; Fitsari, Maziyyi, Wadiyyi da kuma Maniyyi. Wadannan idan suka faru
ko dayansu ya faru to tsarki kawai za'a yi a sake alwala in banda maniyyi, Wanda
shi maniyyi bayan ya bata alwala sai kuma anyi wanka. Sai kuma guda biyu daga
da suke fita daga dubura, sune kuma; Bayangida da kuma tusa. Amma shi
bayan-gida tsarki za'a yi sai a sake alwala, sabanin tusa wacce take ita ba'a
yi mata tsarki alwala kawai za'a sake.
Sai kuma abubuwan da suke sabubbane na
hadasin wadanda yake suna da wasu bayanai, amma su wadancan da zarar ya diga
komai kankantarsa to ya karya alwala inbanda mai fama da cutar yoyon-fitsari,
wadannan abubuwa sune;
(1) Bacci: Shi bacci a nan ya
kasu kashi hudu;
(a) Dogon bacci mai
nauyi, kai tsaye wannan ya karya alwala.
(b) Takaitaccan
bacci mai nauyi, shi ma ya karya alwala.
(c) Takaitaccan
bacci mara nauyi to shi bai karya alwala ba.
(e) Dogon bacci
mara nauyi, bai karya alwala amma an so a sake ta.
Ma'aunin da ake
auna bacci da shi domin a gane yana da nauyi ko ba shi da nauyi shine; Idan ka
san wanda ya zo da wanda ya tashi to baccinka bai yi nauyi ba, amma idan baka
san wanda ya zo ba ko wanda ya tashi ba to baccin ya yi nauyi. Kenan idan kuna
fira sai amma kana gyangyadi sai da ka farka sai kace; ina wane? Ko; wane
yaushe ka zo? To kasan baccinka ya yi nauyi, Allah ya sa mu dace.
(2) Gushewar
Hankali: Idan hankalin mutun ya gushe ta hanyar hauka ko farfadiya ko suma ko
maye to mu sani alwalarsa ta karye. Kenan idan mutum ya yi alwala sai ya hau iska
ko kuma suka yi hadari kawai sai ganinsa ya yi a asbiti ko kuma ya sha ta yi
Marisa-ta sha kafso to alwalar ko wannensu ta karye.
(3) Shafar
Azzakari: Idan mutum ya shafi al'aurarsa kai tsaye tafin hannunsa ya taba
al'aurarsa bawai ta samani riga ko wandoba ko kuma wani kyalleba to malamai sun
karawa juna sani kan makomar al'walarsa, wadansu suke ce kawai alwalarsa ta
karye, wasu kuma suka ce idan ya tabane domin ya ji dadi to ta karye amma idan
ba wai ya yi hakanne domin ya ji dadi ba alwalarsa nanan, wannan maganar kuwa
tana da karfi. Amma dukkanin malamai sun yi ittifaki kan cewa idan ya taba
al'aurarsa ba kai tsayeba ko dai ta saman wando ko saman riga ko saman wani
kyalle to alwalarsa nanan daram.
(4) Shafar
Mace/Namiji: Idan namiji ya shafi mace domin ya ji dadi to ko ya ji
dadin ko bai ji ba alwalarsa ta karye, haka kuma al'amari yake idan mace ta
taba namiji domin ta ji dadi to ta ji dadin ko bata ji ba alwalarta ta karye,
malamai sun kasa shafar zuwa gida hudu;
(a) Idan ya taba
domin ya ji dadi kuma ya ji dadin to alwalar ta karye.
(b) Idan ya taba ba
don ya ji dadi ba sai kuma ya ji dadin to ta karye.
( c) Idan ya taba
domin ya ji dadi sai bai ji da din ba to alwalar ta karye.
(d) Idan ya taba ba
domin ya ji dadi ba kuma bai ji dadinba to alwalarshi tanan daram. Wadannan
bayanai haka mai Ashmawi ya kawosu. Mu sani wadannan bayanai sun shafi macema
idan ita ta yi.
Akwai wadansu da malamai suka karawa juna
sani akan suna karya alwala ko basa karyawa?, wadannan kuma sune:
(5) Shakka Akan
Hadasi: Idan mutum ya tabbatar da alwalarsa sai kuma yake kokwanto ya yi hadasi
ko bai yi ba? Kenan bashi da tabbas? Wasu malamai sukace; Ai da ya yi kokwanto
alwalarsa ta karye domin ba'a sallah da wani abu na shakku. Wasu malaman kuma
suke: Idan ya tabbatar da yana da alwala sai daga bayane yake shakka to ai
shakka bata ture abinda yake dahir, saboda haka sukace alwalar nanan, Allah
shine masani.
(6) Ridda: Shine mutum
musulmi ya kafirta (Allah Ya tsaremu). Wadansu malamai sukace da zarar ya bar
musulunci to da zarar alwalar ta karye, wasu malaman kuma sukace; A'a, ai
ayyukansa da ya yi ba za su baciba sai
in ya mutu bai dawo musulunci ba, wadda alwala na cikin wadannan ayyukan. Mafi
kyawu ga wadannan abubuwa mutum ya sake alwalar shi yafi.
Alwala bata baci idan mutum ya yanke farce
(Kunba), ko ya taba marenansa ko duburarsa ko anyi masa kaho ko ya yi dariya ko
amai ko kuma tuntube har jini ya fita duk alwala bat abaci saboda wadannan, ko
mace ta shafi gabanta amma idan ta sa yatsa a ciki to wasu sunce alwalar ta
karye. Idan mutum yana jin fitsari ko tusa ko bayan gida abinda musulunci ya
karantar shine mutum ya je ya biya wannan bukatar ta shi tukunna, maimakon ya
matse.
Kammalawa:
Alwala tana da muhimmanci matuka saboda haka a kiyayeta a san kuma abinda yake
warwareta, kuma wannan yake nuna mana cewa tunda har alwala za'a ce akwai
abubuwan da suke warwareta dudda ga laima a jikin mutum amma ace alwalarsa ta
warware to lalle yana da kyau musan kuma abubuwan da suke warware musulunci
domin kullun mutum ya dinga ba addininsa kariya ta yadda kada ya warware, Allah
yak are mana addinimmu, amin.
Aliyu Muhammad Sadisu,
Kwakungu, Minna Jahar Neja, Nijeriya.
Za'a iya tuntuba a (+234)08064022965,
ko kuma a: e-mail:aliyusadis@gmail.com
Ko a ziyarcemu a yanar gizo, a :
htt:// munbarin-musulunci.blogspot.com
Jazakallah khairan
ReplyDeleteAllah ya biya ku da aljanna
ReplyDeleteMALAN da allah nomber NA wahatpp pls
ReplyDeleteAllah yasaka da Alheri
ReplyDeleteJazakallahu khairan
ReplyDeleteAllah ya saka da alkhairi mallam
ReplyDeleteAllah yasakada alkhairi
ReplyDelete