Gabatarwa: Alwala ibadace mai zaman kanta wacce Allah madaukakin sarki ya sahar'antata kafin gabatar da wadansu ibadu musammamma sallah, mutum yana samun cikakken ladan alwala idan ya yi ta cikakkiya, Allah madaukakin sarki ya saukar da hukunce-hukuncen alwala a cikin littafinsa mai girma alkur'ani:
'' Ya ku dukkanin
wadanda suka yi imani, idan kuka ta shi za ku yi sallah to ku wanke fuskokinku
da hannayanku zuwa gwiwar hannu ku kuma shafa kawunanku da kafafanku zuwa idan
sawu (idan kafa)…'' Suratu Ma'ida, aya ta:6.
Tabbas wannan aya
ta ti bayanin wajibcin alwala lokacin da za'a yi sallah, kuma ta bayyana gabban
da ya zama wajibi anwanke ko kuma anshafa, sannan kuma ayar ta iya kance ko
wanne mahalli, sannan kuma Ma'aikin Allah –Tsira da amincin Allah su tabbata a
gareshi- ya bayyana siffar yadda alwalar take da maganarsa da kuma aikinsa
bayanin da yake gamsasshan bayani.
Ka sani lalle ita
wannan alwala tanada falala da kuma sharudda da kuma farillai sannan tana da
sunnoni da kuma mustahabbai, sharuddannan da farillai tabbas a tabbata ansame
alokacin gabatar da alwala iya gwargwado domin da sune alwala zata zama
karbabbiya, amma su sunnoni da mustahabbai suna cika alwalarne ta inda
matsayinsu bai kai matsayin sharuddai da farillaiba.
Falalar Alwala: Dudda cewa alwala
wajibice wannan kadai ya isheta samun matsayi a musulunci domin dukkan abinda
akace farillane to wannan matsayi ne me zaman kansa, bayan hadisi na 62 a cikin
Muwadda'u Malik yana cewa: '' An karbo daga Abdullahi As-Sunaabihi, lalle
ma'aikin Allah –Tsira da amincin Allah su tabbata agareshi yace:
''Idan bawa mumini ya yi alwala sai ya yi
kuskurar baki dukkanin laifukan dake bakin sun fice, idan kuma ya face laifukan
(Day a shaka) sun fice, to idan kuma ya wanke fuskarsa laifukan da ke fuskar ta
sa sun fice, har wadanda ke karkashi girar shi, idan ya wanke hannayansa
laifukan dake hannayansa sun fice, har wadanda ke karkashi faratansa (jam'in
farce), to idan kuma ya shafi kanshi laifukan dake kan nashi sun fice har
wadandake kunnuwansa, to idan kuma ya wanke kafafuwansa duk laifukan dake
kafafuwan nasa sun fice, har wadanda ke karkashi farcen kafafun nashi. Sannan
kuma tafiyar da ya yi zuwa masallaci ya zama wani karine da yake da shi''.
Lalle
wannan bakamar falala bace da alwala take da shi, domin mai alwala zai kasance
yana kammala alwala zunubanshi suna digewa a kasa, amma gudu ba hanzariba
wannan ladan zai tabbata ne ga wanda ya yi alwala da shara'a ta tabbatar da ita
ba wacce ya tsinta a kan titi ba.
Sharuddan Alwala: Sharuddan alwala
sune abubuwan da ake so mai alwala ya cika su kafin ya fara alwalar, sune kamar
haka:
(1) Musulunci,
kenan idan wanda ba musulmiba ya yi alwala bata yi ba.
(2) Hankali, idan mahaukaci ya
yi alwala itama bata yi ba.
(3) Wayau, idan
dan karamin yaro mara dabara ya yi bata yi ba.
(4) Ruwan ya zama
mai tsarki, idan ya zama ruwane mara tsarki to alwalar bata yi, bayanai sun
gabata akan hukunce-hukuncen ruwa.
(5) Ruwan ya zama na halas, idan ruwane
da mutum ya sata ko ya same shi bata shar'an tacciyar hanyaba to alwalar bata
yi ba.
(6) Ya kasance mai tsarki, idan
mai alwala ya kasance ya yi fitsari ko bayan gida misali wato ya kasance mara
tsarki kafin alwala to ko ya yi alwalar bata yi ba.
(7) Gusar da duk
abinda zai hana ruwa shiga, kenan idan mutum ya kasance yaba sanye da wani
abunda zai hana ruwa ya kai ga fatar jiki to dolene ya cire shi, kamar tabo
(laka)…'.
Farillan Alwala:
(1) Niyyah:
Domin a banbance wanda ya sa ruwa donin
sanyaya jiki, ko domin gusar da datti, duk wannan ba niyyace ta alwalaba.
(2) Wanke Fuska: ita kuma fuska ta
bangaren tsawo tana farawane daga matsirar gashin kai (banda sanko) zuwa
karshen mukamiki, amma ta fuskar fadi tana farawane daga kunnan dama zuwa
kunnan hagu, wannan shine abinda yake amsa fuska, kenan dole mai alwala ya
tabbatar ko ina ya sami ruwa kamar kasan haba, gefan ido da gefan kunne da
matsa-matsin karan hanci, ayi hattara sosai domin wasu alwalarsu kamar alwalar
yarace.
(3) Wanke Hannaye
Zuwa Gwiwar Hannu. Mai alwala mace ko namiji ya tabbata ya wanke hannayansa
tun daga saman yatsunsa (farce-akaifa) harzuwa gwiwar hannu ya tabbata gwiwar
ta shiga inda ya wanke, anamma akwai manya masu alwalar yara.
(4) Shafar Kai: Ka tabbata ka hada
yatsunka sannan kuma ka fara shafar daga goshi (daidai matsirar gashi) sannan
ka shafa zuwa keya.
(5) Wanke Kafa: Hakanan mai alwala
ya tabbata ya wanke kafarsa harzuwa idon sawu, wato wadannan kasusuwan guba
biyu dake gefan kafafuwa sun shiga cikin inda aka wanke.
(6) Cudanyawa: Mai alwala ya
tabbata ya cudanya duk inda ya wanke ya dirza ruwa ya shiga ko ina.
(7) Yinsu Baidaya: Abinda ake nufi
shine alokacin da ka fara alwala to ka dakatar da komai sai ka kammala, amma
kana alwala kana kuma wata sabga daban wannan bai yi ba.
Mai alwala ya tabbata ya gabatar da wadannan
ayyuka a lokacin da yake alwala ta yadda idan aka rasa daya daga cikin su to
alwalarsa ta shiga hadari.
Sinnonin Alwala:
(1) Wanke Hannaye
Kafin A Tsoma Su A Ruwa. Ta yadda mai alwala zai karkato butar alwala domin ya
wanke hannayansa zuwa Ku'u wato wuyan hannu.
(2) Kuskurar Baki: mai alwala ya
tabbata ya sanya ruwa a bakinsa sannan kuma ya kada ruwan a baki, wannan shi
ake kira da kuskurar baki.
(3) Shaka Ruwa: Shine mai alwala
ya shaki ruwa ruwan ya shiga hancin sa sosai, sai dai kawai idan yana azumine
sai yayi kadan. Amma yadda mutane suke shafar hancinsu wai da sunan shaka ruwa
wannan baiba.
(4) Facewa: mai alwala zai
shaki ruwanne da hannun dama sai ya sa hannun haku akan karan hancinsa, sannan
sai ya fyato ruwan da ya shaka.
(5) Shafar Kunne; Mai alwala ya
tabbata ya shafi cikin kunnensa da wajan kunnan, zaka/ki sanya yatsanka
'yar-manuniya a cikin kunnan sannan ka babban yatsa a wajan kunnan sannan sai
ka shafa, Dirkashi!.
(6) Sake Taba Ruwa: Alokacin da zaka
shafi kunne shin zaka shafi kunnanne da ragowar danshin hannuka da ka yi shafar
kai da shi? Ko ko zaka sake taba ruwa na musamman domin shafar kunne, malamai
sun karawa juna san, ko wanne ka yi ya yi daidai.
(7) Dawo Da Shafar
Kai:
Ka tsaya ka fahimta, ita shafar kai farillace, amma dawo da shafar kai sunnace
daga cikin sonnonin alwala.
(8) Jeranto
Farillai: Ta yadda zaka kawosu daya-bayan-daka kamar yadda aka lissafosu, kada ka
dauki na uku ya zama shine na farko sannan ka biyo shi dana biyar, misali…'.
Wadannan matsayisu
bai kai matsayin farillaiba, amma suna cikin manyan abubuwan da suke cika
alwala.
Mustahabban Alwala:
Wannan shi ke biye
da mataki na sunnoni, kenan sunnoni sun fi mustahabbai karfi, wadanda suke
dukansu biyun farillai na gabansu, babu daya daga cikin sunnoni ko mustahabbai
da mutum zai yi sakaci da su, domin kowannanmu so yake ya yi ibada cikakkiya
kammalalliya, to ko tunda hakane bai kamata yace ai wannan mustahabbine ya
daukeshi kamar wani kankanin abu.
Su mustahabban alwala suna da yawa, amma
yanzu ga kadan daga cikinsu:
(1) Anbaton Allah yace ''Bismillah'',
adaidai loakcin da zaka fara alwala, amma idan mutum ya manta saida yake
tsakiyar alwalar ya tuna bakomai sai ya yi a lokacin.
(2) Addu'a bayan kammala
alwala, itace kuma kamar haka:
أَشْهَدُ
أَنْ لاَ إِلَهَ إِلاَّ اَللهُ وَحْدَهُ لاَ شَرِيكَ لَهُ، وَأَشْهَدُ أَنَّ مُحَمَّدًا
عَبْدُهُ وَرَسُولُهُ، اَللَّهُمَّ اَجْعَلْنِي مِنَ اَلتَّوَّابِينَ، وَاجْعَلْنِي
مِنَ اَلْمُتَطَهِّرِينَ.
Ma'ana: ''Ina shaidawa da babu abinbauta da
cancanta sai Allah, kuma shi kadai yake bashi da abokin tarayya, kuma ina
shaidawa lalle (Annabi) Muhammad bawan Allah ne kuma manzansa ne, Ya Allah ! ka
sanya ni daga cikin masu yawan tuba, kuma ka sanya ni daga masu neman
tsarkaka.''
(3) Karanta Ruwa: Bawai ana nufin
mai alwala ya shasshafa gabbansa bane, a'a, ana bukatar ya yi anfani da ruwa
amma kada ya malalar da shi, domin yana daga cikin tsarin musulunci tattali da
tsimi da tanadi.
(4) Gabatar Da
Asuwaki: Bayani kuma dama ya gabata akan asuwaki, ana yi da danye ko da
busasshe, idan bai samuba sai ayi da yatsa, amma mu sani asuwaki daban kuskurar
baki ma daban. Hakanan kuma ko da mutum lokacin sallah ya yi kuma amma yana da
alwala to abinda ake so shine ya yi asuwaki.
(5) Wuri Mai Tsarki: An so inda zaka
yi alwala ya zama wurine mai tsarki.
(6) Dama Kafin Hagu: abin nufi shine
ka fara wanke hannun dama kafin hannun hagu, hakanan ka fara wanke kafar hagu
kafin ta dama.
(7) Jerantawa:
Wato jeranta kowacce sunnah tare da 'yar-uwarta, kamar fara gabatar da kuskurar
baki kafin shaka ruwa.
(8) Wankewa Sau Uku: Ma'ana wanke
wuraran da ake wankewa sau uku, mu sani wankewa sau uku zai zama mustahabbine
idain wankewar farko ta game ko ina, amma idan ta farko bata gamaba to ta biyu
tananan amatsayin wajibi, haka namma idan ta biyun idan bat agama ba to ta uku
tana nan a matsayin wajibi. Ya zama wajibi mai alwala mace ko namiji ya kula
sosai ya cuccuda inda ya kamata ya sa ruwa ba tare da barnaba. Amma shi kais au
daya ake shafarsa, ba'a shafar kai sau uku. Sannan kuma mutum ya tabbata a
wadannan wankewa da akace ya yi sau uku bai kara akan hakan ba, ya yi iya
kokarinsa ya ga guda ukun sun kammala.
Wadannan kadan kenan daga cikin mustahabban
alwala, kuma wadannan bayanai sun mata kamar yadda suka shafi maza, sai dai
mata su sani gashin kansu da sangalin hannuwansu duka al'aurane, saboda haka
bai halatta su bayyanar da su ga maza, ken an idan zaki yi alwala sai ki sami
wuri ki kawwame kanki.
Wadannan bayanai da suka gabata zasu haskaka
mana yadda alwala take, amma hanya mafi sauki shi ne a yi maka ita a aikace ka
gani domin haka sahabban ma'aikin Allah suka yi, an tambayi Usman dan Affan dan
gane da alwala sai yasa aka kawo mishi butar alawala ya yi musu ita a aikace,
yace kuma irinta ma'aikin Allah ce.
Anan nake kira ga dukkanin limamai na juma'a
dana sauran masallatai da kuma malamai a jami'oi da kwalejin ilimi da kuma
malamai a sakandare da firamare da malaman islamiyyu da malamai masu karantarwa
a masallatai da masu wa'azi da sauran wadanda abin ya shafa da su karantar da
mutane ita wannan alwalar a aikace kowa ya gani ya kuma yi tambaya, kada ka ga
kamar kowa ya gane da zarar ka yi ta a aikace zaka ga abin mamaki, ni na taba
gwada hakan, ita ibada sai an koyawa mutum ba wai daka kawai shikenan ya iyaba,
ko kuma ai shi iyaye da kakanni duk musulmai ne sabo da haka ba sai ya koyaba,
duk wannan maganace ta wanda yake nesa da makaranta, kai da ganin alwalar wani
kasan bai je makaranta ba, Allah ya karba mana ibadummu.
Kammalawa: Lalle wadannan bayanai sun
kara tabbatar mana ashe alwa abace da sai an tashi tuku domin a koyeta tana da
falala da kuma sharudda sannan ga farillai da sunnoni da kuma mustahabbai,
lalle ka nana bukatar malamai daga kowanne bangare su tashi tsaye su karantar
da al'umma wannan ibada a aikace, domin a gudu tare a tsira tare.
Aliyu Muhammad Sadisu,
Minna, Jahar
Neja Nijeriya.
Za'a iya tuntuba a (+234)08064022965,
ko kuma a: e-mail:aliyusadis@gmail.com
Ko a ziyarcemu a yanar gizo, a :
htt:// munbarin-musulunci.blogspot.com
allah ya saka alkahiri
ReplyDeleteAssalamu Alaikum Malam, gaskiya ina matukar farin ciki da fatan alheri gareka akan wannan Kyakyawan aiki... Jazakumullahu Khair!
ReplyDeleteAllah ya saka da alhairi. Ya kuma kara ilimi. Ameen
ReplyDeleteJzkl
ReplyDeleteJzkl
ReplyDelete