Yiwa Mace Mumina
Kazafi: A yanzu za mu yi bayani akan abu na bakwai kuma na karshe
cikin abubuwa bakwai da Ma'aikin Allah – tsira da amincin Allah su tabbata a
gareshi- ya lissafa cikin abubuwan da suke halakar da wanda yake ta'amuli dasu
, wannan abu shine Yiwa Mace Mumina Kazafi.
Kazafi Shine: Jifan mutum da
aikata alfasha ta zina, ko kore juna biyu ko ma Da ba tare da ya bayar cikakkun
shaiduba.
Alokacin da mutum
ya jefa kanshi cikin irin wadannan halayya ta kazafi to lalle ya jefa kansa
cikin halayyar da take halakarwa, domin yin kazafi ba karamin bala'ibane,
alokacin da mutum ai wance mazinaciyace ko ya yi lalata da ita, ko wannan
ciknnanata bana mijintabane ko danta/'yarta ai bana mijinta bane to lalle ya
tsokano tsuliyar dodo dole ya kawo cikakkun shaidu na mutane hudu maza musulmai
da zasu bada shaida akan hakan, idan kuma mai kawo shaiduba ko ya kawo basu
cikaba to kowanne mutum gada cikinsu bulala tamanin (80) za'a yi masa, kamar
yadda bayanai zasu zo nan gaba kadan.
Wannan shiri da musulunci yake dashi
bakaramin shiri bane domin kare mutunci, masu iya Magana na cewa mutunci madarane
in ya zube bai kwasuwa, addinin musulunci yana daga cikin manyan manufofinsa
kare mutunci, wannan yasa musulunci ya dauki irin wannan mataki musammamma 'ya
mace, domin alokacin da aka bata mata suna to gaba daya anbata mata rayuwarta,
shi yasa ayoyin da suka yi Magana akan kazafi sun anbaci macece basu anbaci
namijiba wannanko ba wai dan hukuncin ya sha daban bane a'a hukuncin iri dayane
ga duk wanda ya yi mace ko namiji kazafi, kuma bai iya kawo cikakkakun
shaiduba, idan ko ya kawo shaidu da duk abinda Shara'a ke bukata suka cika to
baza'a kira wannan da sunan kazafiba.
Yiwa mace mumina kazafi bai halattaba kuma
yana cikin abubuwan da suke halakarwa, saboda haka dadin fira ko kiyayya kada
ta dauki mutum ya yiwa wata/wani kazafi ko yasa a yi.
Ayoyin Da Suka Yi
Magana Akan Kazafi: Idan ka tsaya ka kalli ayoyin zaka gansu kashi ukune kuma
duk suna cikin Suratun Nur.
Kashi Na Farko: Ayata: 4-5, Allah
Madaukakin sarki yana cewa: ''Wadanda suke jifan mata masu kamunkai (da
zina) sannan kuma basu kawo shaidu huduba to ku yi musu bulala tamanin (80),
kuma kada ku sake karbar shaidarsu har abada, kuma waddan sune fasiakai. Saidai
kawai wadanda suka tuba bayan haka kuma suka kyautata to lalle Allah mai yawan
gafarane kuma mai yawan jinkai.''
Anan Allah madaukakin sarki ya bayyana
hukuncin duk mutumin da ya yiwa mace/namiji kazafi kuma bai iya kawo shaidu
huduba sai Allah ya bayyana hukuncin da za'a yi masa. Abu na farko bulala
tamanin (80), abu na biyu ba za'a sake karbar shaidarsaba har'abada, abu na uku
kuma wannan mutumin fasikine. Sai idan ya tuba, to ananne malamai suke maganar
shin inya tuba za'a ci gaba da karbar shaidarsa kuma shikenan shi ba fasiki
bane? Amma ko ya tuba sai an yi mishi bulala tamanin.
Kashi Na Biyu: Ayoyin da suka yi
bayanin maigidan da ya yiwa matarshi kazafi kuma bai iya kawo shaiduba to shi
tsinuwa za su yi da matar ta shi, Allah Yana cewa:
''Wadanda kuma suke jifan matansu (da zina) kuma ya kasance
basu da shaidu saidai karankansu, to shaidar dayansu (itace) Rantsuwa hudu da
Allah lalle shi yana cikin masu gaskiya * (Rantsuwa) ta biyar tsinuwar Allah ta
haukanshi in ya kasance cikin makaryata. * Kuma abinda zai hana ayi mata azaba
(haddi) shine ta yi Rantsuwa hudu da Allah cewar lalle shi (mijin) yana cikin
makaryata *. (Rantsuwa) ta biyar lalle fushin Allah ya tabbata akanta in (mijin
nata) ya kasance cikin masu gaskiya'' Surartun Nur, ayata: 6-8.
Anan Allah madaukakin sarki ya yi bayanin idan miji ya yiwa matarshi
kazafi kuma bai iya kawo shaidu huduba to 'Li'ani'' za su yi. Amma duk wanda ba
miji bane to kodai ya kawo sahaidu mutane hudu maza musulmai ko kuma ayi mishi
bulala tamanin, ba maganar shi wanda aka yiwa kazafi wai ya rantse idan ba haka
bane, ko kuma shi da ya yi kazafin cewa ya rantse duk babu kodai shaidu ko
bulala tamanin.
Kashi Na Uku: Ayoyin da suka yi Magana akan kazafin da
aka yiwa mata muminai masu kamunkai natsattsu kammalallu to wadannan masu yiwa
irin wadannan matan kazafi tsine musu aka yi duniya da lahira. Allah madaukakin
sarki yana cewa:
''Lalle dukkanini wadanda
ke jifan mata masu kamun kai gafalallu (daga aikata dukkanin alfasha) wadanda
suke muminai to an tsine musu a duniya da kuma lahira, kuma suna da azaba
maigirma* Aranar da harsunannu za su bada shaida akansu da hannayansu da kuma
kafafuwansu ta sanadiyyar abinda suka kasance suna aikatawa* Awannan ranarce
Allah zai cika musu sakamakonsu na gaskiya, kuma zasu sani lalle Allah shi
wanda yake mai gaskiya kuma mai bayyanar da abubuwa''. Suratun Nur,
ayata: 23-25.
Wannan ya nuna mana shi karankanshi kazafin ya kasu kashi-kashi, kashi
na farko shine yiwa gama garin mutane wadanda suke suna da kyawawan halaye da
kuma wanda ba'a rasaba, su aka anbaci hukunci yi musu kazafi a kashin farko,
sai kuma wanda ya kasance tsakanin miji da mata. Sai wannan kashi na uku, wanda
mutum zai ga mace/namiji mai kamun kai mai addini natsattse mumini kawai ya
antayo ashar ya watsa mata/mashi ya dinga fadan wasu maganganu wanda da za'a
tara mishi arzikin duniya domin ya kawo shaida akan haka ba zai iyaba. Domin
wani ya dauka irin halin da yake dashi to kowa haka yake, to kaga bayan ya kasa
kawo wadannan shaidu za'a yi masa hukuncin kazafi anan duniya sanna kuma ya
jira ranar alkiyama, domin Allah baya bari a taba bayinsa na kwarai, Ya Allah
ka samu daga cikinsu, ka karemu da sharrin masharranta ka tsaremu ka tsaremana
imanimmu, amin.
Kammalawa: Daga takaitattun bayananan ya bayyana
agaremu yadda musulunci ya dauki mutunci da daraja da kima ya karewa kowa
mutuncinsa musamman 'ya mace, domin idan ba hakaba sai kowa ya fadi abinda ya
ga dama ko asashi ya fada yana ganin bai huce aci tararshiba, amma idan yasan
zai sha bulalane to dole ya naba'a yasan me zai fada, sai yazama yak are
mutuncinsa dana zuriyarsa kamar yadda yak are mutuncin wani dana ziriyarsa.
Annanne kuma muka zo karshen wannan silsila wacce take dauke da sharhin
wannan hadisi da Abu Hurairata ya ruwaito daga wurin Ma'aikin Allah na wadannan
abubuwa bakwai masu halakarwa, lalle ma'aikin Allah ya isar da manzanci kuma
tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi, hakika ta'amuli da wadannan
abubuwa tabbas yana halakarwa kuma wannan kowa ya gani ya tabbatar wannan zai
kara imanine bisa imani. Akaro na gaba zamu kawo bayanne kuma wadanda zasu
haskaka mana rayuwarmu da addininmu, Allah ya kaimu wannan lokacin ya hadamu da
imani, aimn.
Aliyu Muhammad Sadisu,
Kwakungu, Minna, Jahar Neja Nijeriya.
Za'a iya tuntuba a (+234)08064022965,
ko kuma a: e-mail:aliyusadis@gmail.com
Ko a ziyarcemu a yanar gizo, a :
htt:// munbarin-musulunci.blogspot.com
No comments:
Post a Comment