Friday, May 3, 2019

0034. HUKUNCE HUKUNCEN AZUMI

Da sunan Allah mai yawan rahama mai yawan jinkai, tsira da amincin Allah su tabbata ga Annabi  Muhammad, da iyalansa da sahabbansa baki daya. Bayan haka:
 A wannan lokacin kuma za mu yi bayani ne akan abinda ya shafi hukunce hukuncen azumi, kama daga ta’arifinsa da kuma falalarsa da kuma nau’ukansa, da sauran bayanai da za su zo akan abinda ya shafi hukunce hukuncensa, da fatan Allah ya yi mana jagora ya kuma datar da mu ya anfanar da mu.
AZUMI.
Idan aka ce azumi a hausa to shi ake cewa (SWAUMU/SWIYAMU) da larabci, a larabci idan aka ce ((Swam)) To ana nufin kamewa ne, amma a shar’ance shi ne:

هو الإمساك عن شهوتي البطن والفرج يوما كاملا بنية التقرب إلى الله تعالى قبل الفجر أو معه في غير زمن الحيض والنفاس وأيام الأعياد.

Ma’ana: Shi ne kamewa daga barin sha’awar ciki da kuma farji cikakken yini da niyyar neman kusanci ga Allah, wacce niyyar za’a yi ta ne kafin hudowar alfijr ko daidai lokacin da alfijirdin yake fitowa, ba a lokacin jinin al’adaba ba kuma na biki ba, kuma ba lokacin bukukuwan sallah ba.
SHARHI.
A wannan ta’arifi na azumi yana kunshe da asalin abinda ake bukata daga mai azumi, ta yadda da zarar an rasa daya daga ciki to wannan abin bai zama shar’an taccen azumi, wadannan abubuwa sune kamar haka:
(1) Kamewa daga barin sha’awar ciki. Kenan wanda bai bar sha’awar cikinsa ba, wacce take ko wannan sha’awar ita ce abinci ko abin sha, ko kuma dukkan wani abu da zai zatsaya matsayin abinci ko abin sha to wannan ba shi da azumi. Ba zai taba yiwu wa ba mutum ya ce yana azumi sannan kuma yana cin abinci ko yana shan abin sha ba.
(2) Kamewa daga barin sha’awar farji. Sha’awar farji kuwa ita ce ko dai saduwa wato jima’i, ko kuma fitar da maniyyi ko maziyyi, wadannan abubuwa uku su ne sha’awar farji, kuma duk mai azumin da ya yi daya daga cikin wadannan abubuwa uku wato ya yi jima’i ko ya fitar da maniyyi ko maziyyi mace ko na miji to ba shi da azumi, domin kowanne daya daga cikin su sha’awace ta farji. Kuma Ma’aikin Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce – a lokacin yana bayyana falalar azumi – ya ce Allah madaukakin sarki ya ce:

((الصوم لي، وأنا أجزي به، يدع طعامه وشربه وشهوته من أجلي)). ((رواه البخاري)).

Ma’ana: Azumi nawa ne, kuma ni zan bada sakamakonsa, (mai azumi) yana barin abin cin sa da abin shansa da sha’awarsa saboda ni”. Bukhari ya ruwaito. Domin duk wanda ya fitar da maniyyi ko maziyyi to lalle wannan bai bar sha’awarsa ba.   
(3). Cikakken Yini. Abinda ake nufi da cikakken yini shi ne tun daga hudowar alfijir har zuwa faduwar rana. Idan aka sami gibi akan haka to azumi bai yi ba, domin Allah madaukakin sarki cewa ya yi:

((وكلوا واشربوا حتى يتبين لكم الخيط الأبيض من الخيط الأسود من الفجر، ثم أتموا الصيام إلى اليل)). البقرة

Ma’ana: Kuma ku ci ku sha, har sai silin farin zare ya bayyana daga silin bakin zare na alfijr, sannan kuma ku cika azuminku zuwa dare.” Bakarah.
Wannan ya nuna inda jinin al’ada zai zo mata minti kadan kafin shan ruwa to ba tad a azumin wannan ranar saboda ba ta a zumci yinin ba ki daya ba. Haka kuma inda jinin al’adar zai dauke mata minti kadan bayan fitowar alfijir to haka shi ma yake ba ta a zumin wannan yinin, dalili kuwa shi ne ba ta azumci yinin baki yaba, kuma abinda Allah ya fada shi ne azumtar yinin baki yada.  
(4) Da niyyar neman kusanci ga Allah, wacce niyyar za’a yi ta ne kafin hudowar alfijr ko daidai lokacin da alfijirdin yake fitowa. A wannan gabar akwai manyan abubuwa guda biyu da ya kamata a yi la’akari da su:
Abu na farko; Niyyar neman kusan ci ga Allah, kenan inda mutum zai ki ci ya ki sha saboda bai sami sarari ba ko sabo da likita ya hana shi ya ci ko ya sha…. Duk wannan ba ya sa ya azumi, shi azumi lalle ne sai idan Allah aka nufata da shi, sannan ne yake amsa sunan azumi shar’antacce.
Abu na biyu: Lokacin da za’a niyyar, lalle dukkan wanda zai ta shi da azumi to ya wajaba akan shi ya kudurce niyyar yin azumin azuciyar shi a cikin daren kafin alfijir ya fito ko kuma daidai lokacin fitowar alfijir din, domin da hakanne zai zama ya azumci cikakakken yini, kamar yadda muka yi bayani a ayar da ta gabata ta Suratul Bakarah, sannan kuma ga Hadisi sayyidah Hafsah – Allah ya kara mata yarda - mai dakin Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi:

((لا صيام لمن لم يبيته بالليل)). رواه الترمذي.  ضعيف في رفعه، صحيح في وقفه.

Ma’ana: Babu wani azumi ga dukkan wanda bai kwana da niyyarsa ba da daddare. Tirmi ne ya ruwaito.    
(5) Ba a lokacin jinin al’adaba ba kuma na biki ba, kuma ba lokacin bukukuwan sallah ba. Wannan tsagi na ta’arifin azumi yana bayani ne a kan lokutan da ba’a azumi a cikin su, kuma ko an yi azumin bai yi ba sai an sake kuma an sabawa Allah.
Wadannan lokuta sune kamar haka:
- Lokacin Jinin al’ada, idan mace tana al’ada to ba ta azumi, kuma in ta yi azumin to azumin bai yi ba sai ta sake shi, sannan kuma ta sabawa Allah da Manzonsa.
- Lokacin Jinin Biki (wato jinin haihuwa), idan mace tana jinin biki to ba ta azumi, kuma in ta yi azumin to azumin bai yi ba sai ta sake shi, sannan kuma ta sabawa Allah da Manzonsa. 
- Lokutan Bukukuwan Sallah: Ba’a azumi a ranar karamar sallah ko babbar sallah, duk kuma wanda ya yi azumi a wadannan ranaku to azumin shi bai yi ba kuma ya sabawa Allah da Manzonsa.
Wannan shi ne ta’arifin azumi, sabanin haka to ba azumi ba ne, sannan wannan ya shafi ko wane azumi.
Nau’ukan Azumi.
A zumi ya kasu kashi – kashi, akwai azumin wajibi a kwai kuma wanda ba na wajibi ba.
Azumin Wajibi.
Azumin wajibi shi ne azumin da shari’a ta dorawa mutum, ta yadda idan ya yi wannan azumin to za’a ba shi  lada,idan kuma bai yi ba to zai iya fuskantar ukuba. Azumi na waji bi su ne kamar haha:
1. Azumin watan Ramadan.
2. Azumin Kaffara.
3. Azumin Alwashi.   
Sai kuma azmin da bana wajiba,wanda idan mutum ya yi yana da lada, idan kuma bai yi ba to ba shi da wannan ladan, kuma ba shi zunubi. Kamar:
1. Azumin Ranar Arafat.
2. Azumin Tasu’a Da Ashurah.
3. Azumin Litinin Da Alhamis.
4. Azumin Kwana Uku A Kowanne Wata.
5. Azumi Shida A Watan Shawwal (Sittu Shawwal), Da dai sauransu.
Kammalawa: Adaidai nan za mu dakata, da fatan mun fahimci menene azumi? Menene yake shiga cikin azumin menene kuma ba ya shiga, a karo na gaba za mu kawo bayanai akan hukunce hukuncen nau’ukan azumi, ta yadda za mu fara da Azumin Ramadan.
Aliyu Muhammad Sadisu,
Kwakungu, Minna, Jahar Niger – Nigeria.
+2348064022965.

e-mail:aliyusadis@gmail.com  

3 comments:

  1. Last Shelter: Survival is a management, builder, and survival multiplayer game where you playclick here the role of a commander of a newly built settlement in a zombie ...

    ReplyDelete
  2. Allah ya saka wa Malam da alkhairi

    ReplyDelete
  3. Masha'allah nima na amfana daga nan Majia Jahar Jigawa

    ReplyDelete