Sunday, May 5, 2019

0036. HUKUNCE HUKUNCEN AZUMIN RAMADAN (2).

                                      GANIN WATA

Da sunan Allah mai yawan rahama mai yawan jinkai, tsira da amincin Allah su tabbata ga Annabi  Muhammad, da iyalansa da sahabbansa baki daya. Bayan haka:

 A daidai wannan lokacin kuma muna son ci gabaa ne da bayani akan hukunce hukuncen azumin watan Ramadan, kama daga abinda ya shafi ganin wata da sauran bayanai da za su zo akan abinda ya shafi hukunce hukuncensa, da fatan Allah ya yi mana jagora ya kuma datar da mu ya kuma anfanar da mu.
Allah madaukakin sarki Shi ne wanda ya wajabta azumin Ramadan, inda ya ce a cikin Suratul Bakara:

((يا أيها الذين ءامنوا كتب عليكم الصيام كما كتب على الذين من قبلكم لعلكم تتقون * أياما معدودات....)). البقرة.

Ma’ana: “Ya ku wadanda suka yi imani! an wabta muku azumi kamar yadda aka wajabtawa wadanda suka zo kafinku, domin hakan zai sa ku ji tsoron Allah. Wasu kwanaki ne kididdigaggu….” Bakarah.

Sai kuma Allah madaukakin sarki ya bayyana wadannan kwanaki da suke kididdigaggu, a inda ya ce:

(( شهر رمضان الذي أنزل فيه القرآن هدى للناس وبينالت من الهدى والفرقان، فمن شهد منكم الشهر فليصمه)). البقرة.

Ma’ana: “Watan Ramadan ! wanda aka saukar da Alkur’ani a cikinsa, shiriya ce ga mutane, kuma bayanaine na shiriya da kuma rarrabewa, to duk wanda ya halarci watan (na Ramadan) daga cikinku to ya azumce shi”. Bakarah.
Sai Ubangiji mai girma da daukaka ya sanya watan da za’a yi azumi a cikinsa shi watan Ramadan, sai kuma Ma’aikn Allah – tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -:

((صوموا لرؤيته وأفطروا لرؤيته، فإن غم عليكم فاقدروا له)) وفي روية ((فأكملوا شعبان ثلاثين)). رواه البخاري ومسلم.

  Ma’ana: “ Ku dauki azumin idan kun ganshi (jinjirin watan Ramadan) kuma ku ajiye idan kun ganshi (jinjirin watan Shawwal), idan an shamakance muku shi to ku cika”. A wata riwayar “Ku cika Sha’aban kwana talatin”. Bukhari da Muslim suka ruwaito.

SHIGAR WATAN RAMADAN.

A wannan hadisi da ya gaba ya bayyana a fili hanyoyin shigar watana Ramadan guda biyu ne:

Hanya Ta Farko: Ganin jinjirin watan Ramadan a lokacinda Sha’aban yake da kwanaki ashirin da tara.

Hanya Ta Biyu: Cika lissafin watan Sha’aban kwana talatin, idan ba’a jinjirin watan na Ramadan ba a lokacin da Sha’aban din yake da kwanaki ashirin da tara.
Idan ya zama an ga jijirin watan Ramadan, kuma wadanda alhakin sanarwa ya hau kansu suka sanar to ya zama waji kowa ya dauki a zumi.

Ya halatta a yi anfani da na’urar kawo nesa kusa domin neman wata, domin dai koda wacce na’ura aka yi anfani ba za’a ganshi ba sai idan shi jinjirin watan ya fito.

Amma idan mutum ya ga wata kuma shugabanni ba su karbi ganinsa ba to shi ne ya zama wajibi akan sa ya dau azumi, ko iyalansa da ‘ya’yansa da almajiransa ba zai sa su su dauka ba, domin hakan ba huruminsa ba ne. kuma ba wajibi ba ne idan ka ce ka ga wata dole sai an yarda ganinka.

Ba’a yin anfani da Calendar wajan tabbatar da shigar watan Ramadan ko fitarsa, misali inda Kalanda za ta nuna cewa Sha’aban kwana ashirin da tara zai yi, sai kuma muka duba wata a ranar ashirin da taran ba mu ganshi ba, to lalle ya wajaba mu cika Sha’aban talatin, mu saki lissafin kalanda. Magana dai anan ita ce kodai aga wata koda ta hanyar na’ura ne ko kuma a cika shi kwana talatin.

YIININ KOKWANTO (YAUMUS SHAKKI).

Idan ba’a ba a ga watan Ramadan ba, a yini na ashirin da tara ga watan Sha’aban to yini na talatin ga watan Sha’aban shi ne yinin kokwanto. An kira shi da yinin kokwanto ne domin ana kokwanton wannan yinin talatin ga Sha’aban ne ko kuma daya ga Ramadan, idan ya tabbata anga watan Ramadan a ranar ashirinda tara ga Sha’aban to ka ga washegari ya zamadaya ga Ramadan kenan kai tsaye. Indai bai tabbata anga watan Ramadan a ranar ashirin da tara ga watan Sha’aban ba, to lalle washe gari tanan a ranar kokwanto, saboda kodai ta zama daya ga Ramadan ko kuma talatin ga Sha’aban, domin hakan ne kuma ake kiran ranar da ranar kokwanto, wanda da Larabciake kira da (Yaumus Shakki).

AZUMI A RANAR KOKWANTO.

Bai halatta a yi azumi anar kokwanto domin a lissafishi cikin na Ramadan, idan mutum ya dauki azumi a ranar kokwanto da niyyar in an ga wata to azumin na Ramadan ne, idan kuma ba’a ga wata to azumin na nafila ne to shi ma a irin wannan hali ba shi kowanne daya daga cikin su, bas hi na Ramadan kuma ba shi da na nafilar.

WURARAN DA BA SU DA RANA.

A kwai wadansu kasashe da ba kasafai rana take bayyana musu ba, akwai kasashen da rana takan bace na tsawon watanni ba ta fito ba, haka kuma idan ta fito ta kan jima ta tsawon watanni bata fadi ba. Abinn da malamai suka bada fatawa akan irin wadannan kasashe shi ne za su yi aiki ne da ganin watan kasashen da suke kusa da su, da su rana take fito musu ta kuma fadi.

DAUKAR A ZUMI DA KUMA AJIYESHI.

Hukuncin kowanne mutum wurin daukar da azumi da kuma ajiye azumin shi ne hukuncin inda yake a lokacin dauka da kuma lokacin ajiyewa. Misali idan lokacin daukar azumi ya yi kana Nijeria to yanzu dole kadauki azumi ko kai dan Nijeriya ko ba dan Nijeriya ba, haka kuma idan lokacin ajiyewa yi.

To yanzu a ce ka dauki azumin daga Nijeriya, sai ka tafi Nijar ko Saudiyyah, sai kuma ya zama Nijeriya ta riga su daukar azumi, amma ga shi yanzu salla ta yi kana wadannan kasashe, to anan hukuncinka shi ne hukuncin wadannan kashashe, za ka ci gaba da yin azumi har sai kasar da kake sun ajiye azumi kafin kai ma ka ajiye, ko da kuma kasar da ka fara azumin su tuni sun yi sallah, sannan haka kuma ko kai naka azumin zai kai talatin da daya ne ko da biyu…’.

Sannan haka hukun cin yake idan kasar da ka fi wacce take ta Musulmaice, amma sun riga ku daukar azumin domin sun riga ku ganin wata, to haka za ka yi aiki da ganinsu, idan sun ga watan sallah a ashirin da tara ga Ramadan a lissafinsu, alhalin kai kuma a lissafinka kana da azumi ashirin da takwas ne ko da bakwai haka zaka ajiye azumin naka, idan an yi sallah sai ka rama wadannan kwanakin. Dalilin da malamai suka bayar akan wadannan matsalili shi ne fadin Ma’aikin Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi:

((الصوم يوم تصومون، والفطر يوم تفطرون)). رواه الترمذي.

Ma’ana: “Azumi shi ne ranar da kuke azumin, sallah ranar da kuke sallah”. Tirmizi ne ya ruwaito. 

Kammalawa: Da wannan ne muka karshen wannan bayani akan abinda ya shafi ganin wata, da kuma abubuwan da suke da alaka da shi.  

Aliyu Muhammad Sadisu,
 Minna Jahar  Neja, Nijeriya.
 Za'a iya tuntuba a (+234)08064022965,
ko kuma a: e-mail:aliyusadis@gmail.com
Ko a ziyarcemu a yanar gizo, a :
htt:// munbarin-musulunci.blogspot.com
        


No comments:

Post a Comment