Saturday, May 4, 2019

0035. HUKUNCE HUKUNCEN AZUMIN RAMADAN (1).


Da sunan Allah mai yawan rahama mai yawan jinkai, tsira da amincin Allah su tabbata ga Annabi  Muhammad, da iyalansa da sahabbansa baki daya. Bayan haka:
 A wannan lokacin kuma za mu yi bayani ne akan abinda ya shafi hukunce hukuncen azumin watan Ramadan, kama daga falalarsa da sauran bayanai da za su zo akan abinda ya shafi hukunce hukuncensa, da fatan Allah ya yi mana jagora ya kuma datar da mu ya kuma anfanar da mu.

FALALAR AZUMIN RAMADAN.
                                      
Azumun watan Ramadan azumin ne da yake da matukar falala, babu wani azumi day a kai shi falala a cikin dukkanin nau’ukan azumi da ake da su, kadan gada cinkin falalar azumin watan Ramadan:
(1) Rukuni ne daga rukunan addinin Musulunci, wato addinin Musulunci bai cika said a azumin watan Ramadan, wanda yake kasancewar azumin Ramadan yana daya daga cikin shika-shikan Musulunci guda biyar ya isheshi falala, Mala’ika Jibrilu ya tambayi Ma’aikin Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi akan menene Musulunci ? sai Ma’aikin Allah ya ce:

((الإسلام أن تشهد أن لا إله إلا الله، وأن محمدا رسول الله، وتقيم الصلاة، وتؤتي الزكاة، وتصوم رمضان، وتحج البيت إن استطعت إليه سبيلا)). رواه مسلم.

Ma’ana: “Musulunci shi ne ka shaida da babu abin bautawa da cancanta sai Allah, kuma lalle Annabi Muhammadu Manzon Allah ne, ka tsayar da sallah, kuma ka bayar da zakkah, ka yi azumin Ramadan, ka yi aikin Hajji idan ka sami ikon haka”. Muslim ne ya ruwaito. Sai wannan ya nuna mana azumin Ramadan daya ne daga cikin shika-shikan Musulunci guda biyar.
(2) Yadda Ma’aikin Allah – tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi – ya fayyace falalar wannan azumin, ya ce: “A aljanna akwai wata kofa babu mai shigarta sai masu azumi”. Kana Ma’aikin Allah – tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi –  ya ce:
((من صام رمضان إيمانا واحتسابا، غفر له ما تقدم من ذنبه)). رواه البخاري.

Ma’ana: “Duk wanda ya azumci Ramadan yana mai imani da kuma neman lada an gafarta masa abinda ya gabatar na zunubinsa”. Bukhari ya ruwaito.

Lalle wannan yana nuna mana irin girma da falala da daraja da azumin watan Ramadan yake da shi, shi ne azumin da yake gaba da kowanne azumin, kana shi ne azumin da ya fi kowanne azumi falala da daraja. Bannan abinda ake so shi ne mutum ya yi wannan azumi na Ramadan yana mai imani da Allah da Manzonsa, yana kuma mai kaunar lada a wurin Allah. Saboda haka koda kana kwadayin yin azumin nafila amma ana binka wani azumin na Ramadan to lalle ilalla shakka babu na Ramadan da ake binka shi zaka fara gabatarwa tukunna, domin shi ya fi kowanne azumi falla, daga nan ink agama ranka wanda ake binka sai ka yin a nafilar da kake son yi.

AKAN WA AZUMIN RAMADAN YA WAJABA?.

Idan watan Ramadan ya kama akawai wadanda azumin ya zama wajibi akan sun an take da zarar an ga wata, akwai kuma wadanda azumin bai haukansu ba anan take, wasu za su rama shi bayan wucewar watan wasu daga cikin su kuma ba za su rama ba, anan za mu yi bayan kowanne.
Wanda azumin watan Ramadan yake wajaba akansa shi ne: “Dukkan wanda yake musulmi, baligi, mai hankali, mai lafiya wanda ba a halin tafiya yake ba”.   

Musulmi: Da muka ce dukkan wanda yake musulmi, kenan an fitar da duk wanda yake ba musulmiba. Azumin Ramadan yana wajaba ne akan musulmi mace ko namiji banda wanda ba musulmi ba. Idan wanda ba msulmi ba ya yi azumi to azumin bai yi ba, sannan kuma idan wanda ba musulmi ba ya musulunta to ba zai rama azumin da ya wuce ba, idan ya musulunta cikin watan Ramadan ne da rana to da zarar ya musulunta sai ya dakatar da cin abin ci da kuma shan abin sha, amma an so bayan azumi ya wuce ya rama wannan guda dayan, na ranar da ya musulunta wannan idan ya musulunta da rana kenan, amma idan ya musulunta bayn shan ruwa ko kafin sahur wannan kai tsaye za’a tashi da shi ne da azumi.

Baligi: Azumin Ramadan na zama wajibi ne akan wanda ya balaga, idan yaran da ba su balaga ba suka yi azumi azumin ya yi, kuma ba zai rama adadin azumin da bai yi ba kafin ya balaga.

Kadan daga alamomin balaga akwai: Fitar maniyyi daga mace ko namiji, bayyanar gashin mara mace ko namiji, jinin al’ada ga mace kadai, ciki ga mace kadai…’’. To da zarar daya daga cikin wadannan alamomi sun bayyana to lalle hukunce hukuncen shari’a sun hau kan mutum ciki kuma har da azumin watan Ramadan, saboda haka sai iyaye da malamai su kula. Domin irin yadda ake barin balagaggun yara ba sa azumi suna ci suna shad a rana, wai ai ba su yi aure ba, ko kuma ai yau suna da aiki a gida ko a gona koma dai a inane wannan ba karamin laifi ba ne.

Mai Hankali: Idan mahaukaci ya yi azumin watan Ramadan to azumin bai yi ba, domin sharadi ne na mai azumin ya zama mai hankali.

Mai Lafiya: Idan mara lafiya ya yi azumi to azumin ya yi, idan kuma ya aji ye azumin to sai ya rama adadin kwanakin da ya sha, babu wani abu akansa bayan haka.

Matafiyi: Shi ma matafiyi iadan ya yi azumin a halintafiyar ta sa to azumin ya yi, idan kuma ya aji ye hakamma ya yi, sai ya rama adadin kwanakin da ya ajiye bayan sallah.

Kammalawa: Da wannan takai taccan bayanin, ya bayyana a garemu yadda falalar azumin watan Ramadan take, da kuma wadanda azumin ya wajaba akan su, kana da hukunce hukuncen haka. 
   
Aliyu Muhammad Sadisu,
 Minna Jahar  Neja, Nijeriya.
 Za'a iya tuntuba a (+234)08064022965,
ko kuma a: e-mail:aliyusadis@gmail.com
Ko a ziyarcemu a yanar gizo, a :
htt:// munbarin-musulunci.blogspot.com


No comments:

Post a Comment