Tuesday, February 4, 2014

ABINDA KE WAJABA GA SABON MUSULUNTA YA YI KO YA BARI


بسم الله الرحمن الرحيم
Dukkan godiya ta tabbata ga Allah, Tsira da aminci su tabbata ga Annabimmu da iyalanshi da kuma sahabbanshi.
   Bayan kaha; Hakika Allah ya halicci halittane domin su bauta mishi, Allah madaukakin Sarki yana cewa; ''Kuma ban halicci aljan da mutumba sai domin su bauta mini''. Kuma ba'a bautawa Allah sai da abinda ya shar'anta, tabbas ya aiko da manzanni domin su yiwa mutane bayanin abinda ya shar'anta, domin bautawa Allah da abinda bai shar'antaba batacciyar ibadace, kuma ya kammala aiko manzanni da manzanshi Muhammad –tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi-, kuma ya wajabtawa mutane binshi, Allah madaukakin sarki yana cewa; ''Kace ya ku mutane lalle ni ma'aikin Allah ne zuwa gareku bakidaya''. Duk wanda bai yi imani da (Annabi) Muhammad ba to ba musulmi bane, kuma addinin (Annabi) Muhammad shine musulunci, Allah kuma bai karbar wani addinin da ba shi ba, Allah madaukakin sarki yana cewa; ''Duk wanda ya bi addinin da ba musulunci ba to ba za'a taba karba daga wurinsa ba, kuma shi aranar lahira yana cikin asararru.
  Shi musuluncin da (Annabi) Muhammad ya zo da shi yana da shika-shikai guda biyar; Shaidawa da babu abin bauta da cancanta sai Allah kuma Muhammad manzon Allah ne, da kuma tsaida sallah, da kuma bada zakkah, da azumin watan Ramadan, da ziyarar dakin Allah mai alfarma tare da ikon hakan (wato aikin Hajji).
Abinda Wanda Yake So Ya Shiga Musulunci Zai Yi:
Zai furta kalmar shahada sannan ya biyo da rukunan musulunci kamar haka;
1. zaice; أَشْهَدُ أَنْ لاَ إِلَهَ إِلاَّ اَللهُ وَأَشْهَدُ أَنَّ مُحَمَّدًا رَسُولُ اَللهِ  , zai furta hakan ne a fili.
2. sai ya sallaci salloli biyar; Asubahi da Azahar da La'asar da Magariba da Isha, a kowanne yini da dare tsawon rayuwa, Asubahi raka'a biyu, Azahar raka'a hudu la'asar raka'a hudu magariba raka'a uku isha raka'a hudu, ba kuma zai yi sallar ba sai bayan ya yi alwala, wannanko zai farune ta hanyar wanke fuska da wanke hannuwa zuwa gwiwar hannu da shafar kai da wanke kafafuwa zuwa idon sawu da ruwa mai tsarki mai tsarkakewa.
3. Idan yana da kudi da ya karu akan bukatarsa sai ya fitar da daya bisa arba'in (2.5 %) wannan zakka ce da zai baiwa talakawa da miskinai a kowacce shekara, amma idan ya kasance yana da dukiyar sai dai ba abinda ya karu akan bukatarsa to anan babu wata zakka da zai fitar.
4. Zai azumci watan Ramadan, shi ne kuma wata na tara a kalandar musulunci (Zaibar abinci da abin sha da saduwa da iayali tun daga hudowar alfijr har zuwa faduwar rana) zai kuma ci ya sha ya sadu da iyalinsa da daddare kadai.
5. Idan ya kasance yana da arziki da kuma lafiyar jiki to sai ya yi aikin hajji sau daya a rayuwarshi, idan ko yana da kudi ne amma bashi da lafiyar jiki saboda tsufa ko wani dadadden rashin lafiya to sai ya wakilta wanda zai je ya yi mishi sau daya.
6. Sauran abubuwan da suka rage na biyayya ga Allah to su cuko ne ga wadannan rukunan.
Abinda Yake Lizimtar Musulmi Ya Bari:
1. Yabar shirka da dukkan nau'ukanta, itace kuma bautawa wanin Allah, akwai daga ciki kiran matattau da yi musu yanka da yi musu alwashi.
2. Yabar dukkanin bidi'o'i, wato ibadojin da Ma'aikin Allah (Annabi) Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi bai shar'anta ta ba domin yana cewa ''Duk wanda ya aikata wani aiki da bamu sa shi ba to ba za'a karba ba''.
3. Yabar cin riba da caca da cin-hanci-da-rashawa da kuma karya a dukkan mu'amalolinsa da sayar da abinci na haram da kayayyaki na haram.
4. Yabar zina wato saduwa da matar da ba ta shi ba a shar'ance ya kuma bar luwadi wato auren jinsi.
5. Yabar shan giya da cin alade da dukkan abinda aka yanka ba domin Allah ba, ya kuma bar cin mushe.
6. Ya kuma bar auren matan da suke kafirai ne saidai in kiristocine.
7. Ya rabu da matarshi da take ba musulmaba sai dai in kiristace ko kuma ta musulunta tare da shi ko ta musulunta kafin ta gama iddah.
8. Idan kaciya ba zata cutar da shi ba sai likitan da yake musulmi ya masa kaciyar.
9. Idan ya kasance zai iya tashi daga garin da bana musulmaiba ne sai ya tashi, idan kuma ba zai iya barin garinba to sai ya zauna a garin nasa ya kuma yi riko da addininsa.
Wanda ya rubuta:
Sheikh: Salih bn Fauzan Al-Fauzan
Mamba a majalisar manyan malamai. (Saudi Arebiya)
19/3/1433
Fassarar:
Aliyu Muhammad Sadisu (Nigeria - +2348064022965)

No comments:

Post a Comment