Thursday, February 6, 2014

019- LOKUTAN SALLAH (1)


Gabatarwa: Wannan wani babine mai girman gaske dudda cewa dukkan wadannan bayanai suna da matukar muhimmanci. Su lokutan sallah saninsu yana da matukar muhimmanci, domin ba'a yin sallah sai lokacinta ya yi kuma ba'a bari lokacinta ya fita ba'a yi ba, asalima shigar lokaci sharadine daga cikin sharuddan sallah kamar yadda bayanai suka gabata kuma mukace da izinin Allah zamu kawo bayanai akan abinda ya shafi lokutan sallah.
Lokutan Sallah: Kowacce sallah daga cikin wadannan salloli wajibabbu guda biyar tana da lokacinta da Allah madaukakin sarki ya iyakance mata ba za'a yi ta kafin lokacinta ya yi idan kuma lokacin ya yi ba za'a bari sai ya fitaba, Allah madaukakin sarki yana cewa '' Lalle ita salla ta kasance akan muminai wajibice kuma abar gayyadewa lokaci'' Suratun Nisa'i, aya ta: 103. Umar dan Khaddab Allah ya kara masa yarda yana cewa 'Sallah tana da lokaci da Allah ya sansa bata inganta sai a wannan lokacin'. Sallah tana zama wajibine idan lokacinya ya shiga kamar yadda ayoyi masutarin yawa suka nuna, gabadayan malamai sun yi ijima'I akan falalar dake cikin yin sallah a farkon lokaci a dunkule, Allah madaukakin sarki yana cewa '' Ku yi rige-rigen aikata alheri'' Bakara, aya ta:148 wanda yake sallah itace babba akan dukkan wani alheri da musulmi zai gabatar.
   Kowacce sallah daga cikin salloli biyar din nan tana da lokacinta da Allah ya kayyade mata wanda kuma ya yi daidai da halin da bayinsa suke, ta yadda zasu gabatar da wadannan salloli a kan lokutansu ba tare da wani abu ya tsare sub a asalima zata taimaka musu ne, kuma ta kankare musu zunubai, ma'aikin Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi ya kamantata da ruwa da yake gudu wanda mutum a kullun yake wanka a cikinsa sau biyar kana tsammanin zaka ga wani datti a tare da shi!.
1. Lokacin Sallar Azahar: Lokacin sallar azahar shine daga lokacin da rana ta karkata daga tsakiyar sama ta koma zuwa bangaren yamma, zaka gane hakane ta yadda inuwarka zata koma bangaren gabas bayan ada baka gantaba. Wato yadda al'amarin yake alokacin da rana take gabas zaka ga inuwa ta na yammane, lokacin da rana take kara dagowa lokacin inuwar take kara ragewa harzuwa lokacin da rana zata zo tsakiyar sama daidai, za kuma tad an tsaya kadan, to adaidai wannan lokacin da take atsakiya cif zaka ga ba wata inuwa, domin sai ranar ta karkata wani bangarene sannan inuwar ta bayyana a wani bangaren. To daga lokcin da ranar ta ci gaba da tafiya zuwa yamma to daga lokacin inuwa zata ci gaba da bayyana bangaren gabas, ranar tana kara yin yamma inuwar tana kara tsawo bangaren gabas. Daga lokacin da ranar ta karkata zuwa bangaren yamma kuma alamar hakan itace ka ga inuwarka ta bayyana bangaren gabas to da ganin haka lokacin sallar azahar ya yi, ba abinda ya rage sai dai a sallah ce ta, sai dai idan lokacin ana fama zafin rana sai a jinkirta kadan, ma'aikin Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi yana cewa:  '' Idan zafi ya tsananta to kudan sanyaya sallah, domin tsananin zafin nan daga nunfashin jahannama ne''. Bukhari da Muslim da Malik a Muwatta'u.
   Wannan shine loakcin sallar azahar har kuma zuwa inuwar komai ta zama kamar tsawonsa.
   Kenan anan ba wata sallah mai suna karfe biyu ko karfe daya, kamar yadda lokuta suke canzawa a tsawon shekara to haka lokutan sallah suke canjawa, duk mun san wani lokaci magariba akan yita kusa bakwai na yamma wani lokacin kuma kusan shida da wani abu na yamma, to ashe kamar yadda muka yarda lokacin magariba yana canzawa to hakanan na sauran sallolin, kuma fa duk wannan a wasu yankunane kadan fa domin inda mutum ya je hajji ko umarah a inda aka saukar da sallar to da yaga wani lokacimma tuni karfe daya an gama sallah kuma da shi aka yi ta, amma idan ya dawo gida yace sai ta nuna.
2. Lokacin Sallar La'asar: Lokacinta yana farawane daga lokacin da inuwar kowanne abu ta zo kamar tsawonsa, kenan inda zaka kafa tsinke a kasa sannan sai ka ja layi a karshen inuwar to daga lokacin da tsawon tsinken ya doru kadan kan inuwar to lokacin sallah ya yi, daga nan har zuwa lokacin da inuwar kowanne abu zata ninka shi sau biyu, amma kada ka manta yinta a farkon lokaci shine abinda ya fi.
   Anan ana samun manyan kura-kurai guda biyu, kuskure na farko shi yafi ko wanne muni shine daukan lokacin sallar la'asar shine: karfe uku da rabi (3:30pm), wannan kuskurene domin dayawa masu irin wannan sallar za su yita tun kafin lokacinta ya yi, kenan basu da sallah domin sun yita kafin lokaci. Kuskure na biyu kuma shine jinkirtata bayan lokacin ya shiga waishi ai yana ganin ance har inuwa ta ninka gida biyu.
3. Lokacin Sallar Magariba: Lokacin sallar magariba yana farawane daga lokaci da kaskon rana ya bace bakidayansa to daga wannan lokacin magariba ta yi ko da ana ganin haske, kuskuren da ke yi anan shine jinkirta sallar har sai dare ya yi alhali kuma lokacinta takaitaccene, daga lokacin da rana ta fadi har zuwa bacewar shafaki, shi kuma shafaki: wani haskene da yake gauraya da ja anan sai jan ya bace ya bar hasken sai shima hasken ya bace.
   An fi so a gabatar da kowacce sallah a farko lokacinta to hakama ita sallar magariba.
4. Lokacin Sallar Isha: Shi lokacin sallar lisha yana farawane daga lokacin da shafaki ya bace, wanda yake shine karshen muhtarin magariba har zuwa kashi daya cikin uku na dare, zuwa nan muhtarin lisha ya tsaya, amman dai lokaci na laruri yana kaiwane harzuwa lokacin da alfijiri na biyu ya kyato, wanda yake kuma shine farkon muhtarin asubahi.
   Shi babban kuskuren da ake samu a sallar lisha shine wasu wuraran sun dauki karfe bakwai da rabi (7:30pm) shine lokacinta wanda yake nuna sauda yawa ana yinta kafin shigar lokacinta.
5. Lokacin Sallar Asubahi: shi  lokacin sallar asubahi yana farawane daga hudowar alfijiri na biyu kuma zai ci gaba har zuwa fitowar rana, saidai kada ka manta anfi so a gabatar da ita da zarar an tabbatar da fitowar alfijir.
   Kuskuren da ake samu a sallar asubahi shine yadda wasu suka maida lokacin shine karfe biyar da rabi na asuba (5:30am) wanda yake wannan babban kuskure domin sauda yawa wasu lokutan alfijir yana fitowane tun kafin biyar, ballema a wasu yankunan, kuma Karin hatsarin akwai masu azumi na nafila ko ramuwa kuma sun dogarane da kiran sallah shi kuma mai kiran sallar bai kiraba gashi kuma alfijir ya dade da fitowa.
   Wadannan sune lokutan sallah kuma idan muka lura zamu ga kowacce sallah tana da lokutai guda biyu; Muhtari da kuma Laruri.
    Muhtari: shine zababban lokaci da aka zaba domin ka gabatar da wannan sallar, ba'a yarda ka shiga lokacin laruriba sai inda larura kuma musulunci ya fayyace me ake nufida larurar, sannan shima muhtarin yin sallah a farkonshi tafi lada da samun matsayi a wurin Allah mai girma da daukaka.
Kammalawa: Atakaitaccan wannan bayani ya bayyana a fili cewar lokutan sallah lokutane da musulunci ya sanya, jindadi da walwala shine abi wadannan lokuta da musulunci ya kayyade, bai al'ummar musulmi su yi wasa da sanin lokutan sallah ba musamman ladanai domin da kiran sallar su ake barin sahur da shi kuma ake shan ruwa. Nan gaba zamu kashi na biyu na lokutan sallah, da izinin Allah.
Aliyu Muhammad Sadisu,
 Minna Jahar  Neja, Nijeriya.
 Za'a iya tuntuba a (+234)08064022965,
ko kuma a: e-mail:aliyusadis@gmail.com
Ko a ziyarcemu a yanar gizo, a :
htt:// munbarin-musulunci.blogspot.com

No comments:

Post a Comment