Wednesday, October 3, 2012

KURAKURAI A KIRAN SALLAH


بِسْمِ اَللهِ اَلرَّحْمَنِ اَلرَّحِيمِ
Gabatarwa:
Dasunan Allah maiyawan rahama maiyawan jinkai, tsira da amincin Allah su kara tabbata ga fiyayyan halittar Allah, manzan tsira Annabi Muhammad da Iyalan Sa da Sahabban Sa baki daya da wadanda suka bi bayansu da kyautatawa izuwa ranar sakamako, amin.
Bayan haka, hakika wannan bita da 'yan uwa suka shirya a Shirin Hasken-Musulunci anan Minna, fadar Jahar Neja ayau (Alhamis: 4, ga Ramadan 1432 daidai da 4, Agusta 2011) lallai tana da matukar muhimmanci musamman a irin wannan lokaci, wanda yake a fili take irin gudun mawar da ladanai suke bayarwa a cikin al'umma baki daya.
          Wannan matashiya da zamu tattauna a kanta maitaken "Kura-Kuran da ake samu a kiran sallah'' muna fatan ta zama wani abune da za mu yiwa juna gyara, don gyara kayanka bai zama sauke mu raba ba, kuma muna so a wannan haduwa ya zana an magance wadannan kura-kurai duddacewa ba su ke nanba, amma har idan muka gane cewa akwai kurakuran kuma muka dauki hanyoyin gyara to zamu sami taimakon Allah akai, Allah ya yi mana jagora amin.
          A cikin wadannan kurakurai akwai wadanda su ke da alaka da maikiran sallah, akwai kuma wadanda suke da alaka da ma'anonin kiran sallah ta yadda idan ma'anar ta canza sai ta maida shi ba kuma kiran sallah ba. Sannan akwai wadanda suke da alaka da al'umma baki daya, lalle wanan yana nuna mana cewa matsayin ladaini a cikin al'umma ba karamin matsayi bane, muna rokon Allah da sunayan kyawawa da siffofin sa madaukaka ya yima jagora amin.
          A yanzu za'a dan lissafa wasu daga ciki, ayi kuma dan karin haske sannan abada shawarwari.
Akwai wadansu abubuwa da zasu shiga cikin kura kuran da ake samu a kiran sallah, kamar:
1. Rashin Kiran Sallah A Farkon Lokacinta: Kamar yadda malamai suka zayyana bayana a littafai cewar kiran sallah shi ne: Sanar da mutane shigar lokacin sallah. Kuma kamar aka sani kowacce sallah tanada lokacinta kuma gashi malam ya kara mana bayi ya kuma fito mana da lokatan fili, wanda rashin kiran sallah a farkon lokacin ta ya haifar da angama kiran sallah sai a tada ikama, wanda anasone tsakanin kiran sallah da tada ikama a sami tazara ta yadda mara alwala zai yi alwala, wanda sai ya yi tsarki ya je ya yi tsarki, anan kenan zamu gane yana daga cikin manyan ayyukan ladan da lokacin sallah ya yi ya kita domin ya sanar da al'umma shigar lokacinta.
          Babbancin kiran sallah da ikama shine: Kiran sallah sanar da mutane shigar lokacin sallah (Ladani kuma shi ya kamata ya fi kowa tantance lokutan sallah), ita kuma ikama: sanar da wadanda ke cikin masallaci anfara sallah.
2. Rashin Tantance Lokaci: Ladani ya sani shi ne mutum na farko da yafi kowa sanin canjin lokaci da yadda yake karuwa da kuma yadda yake raguwa, kuma idan zai yi anfani da agogo kada ya dogara da agogo daya, ya zamana yana dasu uku ko hudu, rashin wannan wadansu ladanan suke kiran sallah tsakaddare ko dab da magariba idan hadari ya rufe rana.
          Ladanifa ya sani sallolin mutane da azuminsu suna ratayene  a wuyanshi, miliyoyin mutane basa shanruwa ko su dakatar da sahur sai ladan ya kira sallah.
3. Rashin Tsayawa A Koyi Kiran Sallah: wannan yana daga cikin manyan matsalolin da ake samu, ta yadda inda za'a kowa ya fadi malamin da ya koya masa kiran sallah to da anyi zuffa. Hakan ya haifar da kowa yake yin yadda ya ga dama, wasuma ka ji da yarukansu suke yi ba da larabciba.
4. Rashin Tantacce Ladanai A Masallaci: wannan yasa kowa ya zama ladani, wanda yake wannan kuwa kuskure ne, wannan baihana a sami ladanai a masallaci gudaba, su zama biyu ko uku ko dai gwargwadon abida ya sawwaka amma tsayyayu, wannan zai sa asan cewa ladani wane yana kiran sallar asubahine kafin alfijiri ya keto amma ladani wane sai bayan alfijiri, kamar yadda ya kasance tsakanin Bilal da Ibnu ummi maktum Allah ya kara musu yarda.
5. Rashin Sanin Ma'anonin Kiran Sallah: wannan ya haifar da abubuwa masu yawa, da basa cikin addini, misali: Ladani ya kammala kiran sallah sai yace 'Ayi alwala, a jaddada' inda yasan ma'anar
حَيَّ عَلَى اَلصَّلاَةِ، حَيَّ عَلَى اَلْفَلاَحِ
Hayya alas Swalah, Hayya alal Falah da bai fadi waccar maganarba.
6. Rashin Kula Da Ladubban Sallah: wannan ya sa sai kaka ladani yana kiran sallah amma sai kaga kamar yana wani abu da bashi da alaka da addini, wani lokacin sai ya yi kamar ya juyawa alkibla baya.
7. Kura kurai a lafuzza: ana samun kurakurai masu tarin yawa a lafuzzan kiran sallah. Wadannan kurakurai sun kashi kashi biyu.
(a) Kuskure mai canza ma'ana: irin wadannan kura-kurai suna fitar da shi daga kiran sallah kwatakwata ya zama wani abu daban, misali:
اَللهُ أَكْبَرُ – أَكْبَارُ
(b) Kuskure na bata lafuzza: wanda yake fitar da shi daga duniyar larabci, misali:
أشْهَدُ أَنَّ مُحَمَّدًا رسولُ اللهِ
Shawarwari:
A takaitaccen wanna jawabi da kuma wadannan abubuwa dana gani ina bada shwara kamar haka:
1. Bayar da mintina bayan kiran sallah kafin tayar da sallah, wannan ko zai tabbatane idan ankira kowacce sallah a farkon lokacin. Misali Azahar minti 20 la'asar minti 15 magariba minti 10 lisha minti 15 asuba minti 20.
2. Ladani ya zama yana da agogo kamar uku banda na wayarshi, kuma ba zaije kiran sallah ba sai ya duba su duka.
3. Aiki da dukkan abubuwan da aka gabatar a wannan bita.
4. Gyara inda duk mutum ya ji yana da kuskure.
5. Isar da wadannan bayanai ga wadanda basu zo wannan bita ba.
6. Ladanai su samara da wata haduwa da zasu dinga yi lokaci lokaci domin tuntubar juna koda ko za'a fara a matakin unguwa unguwa ne.
7. Ci gaba da shirya irin wannan bitar lokaci bayan lokaci
8. Koyon kiran sallah baki da baki daga wurin malamai masana.
          Allah ya gafartamana ya kuma ya fe mana, Allah ya karbi ayyukammu amin summa amin.
وصلى الله وسلم على نبينا محمد وعلى آله وصحبه وسلم
Aliyu Muhammad Sadisu,
 Kwakungu, bayan Ofishin 'Yansanda,
Minna jahar  Neja Nijeriya.
 Za'a iya tuntuba a.
G.S.M. (+234)8064022965.
 e- Imei : aliyusadis@gmail.com
htt:// munbarin-musulunci.blogspot.com
www.fecebook.com/Aliyu Muhammad Sadisu
www.youtube.com/Aliyu Muhammad Sadisu

No comments:

Post a Comment