Wednesday, October 3, 2012

Aikin Hajji A Wannan Shekarar 1433 (2012) Ina Mafita??


Da sunan Allah mai yawan rahama mai yawan jinkai, tsira da amincin Allah su tabbata ga ma'aikin Allah. Bayan haka lalle wannan masifa da ta aukawa kasarnan a wannan gagarumin aiki wanda yake rukunine daga cikin rukunan addinin musulunci abin a tsaya ai nazarinta ne domin aga ta ina ta fito kuma ya za'a tunkareta ta yadda ba zata sake aukuwaba, domin ace mutum ya isa kasa mai tsarki lamilafiya amma kuma a dawo da shi kai wannan ba karamin tashin hankali bane Ya Allah muna rokonka da kada musake ganin maimaituwar wannan al'amari. Kamar yadda na fada lalle ya kamata mu tsaya mu yi wa wannan lamari karatun ta-natsu, mabudin wannan karatu itace ayar dake cikin Suratus Shura aya ta 30. ''Kuma duk abinda ya sameku na kowacce irin masifa to fa saboda abinda kuka gabatarne, kuma (Allah) Yana ga abubuwa masu tarin yawa''.
          Lalle la'akari da wannan ayar yana dakyau mu tsaya muga me aka gabatar da ya haifar da wannan al'amari don asan matakin da za'a dauka don hana aukuwar irinshi nan gaba. Ni a ganina wadannan al'amurra sune kamar haka:
1. Mahrami: Shine mutumin da yake haramunne ya auri matar da yake tare da ita (kamar uba mahramine na 'yarshi, ko kaka ko siriki) shi yasa sai ace mahrami ko miji, Ma'aikin Allah –tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi- yana cewa: Bai halatta ga dukkan matar da tai imani da Allah da ranar lahira da ta yi tafiya kwana guda ba tare da maharraminta ba'' Hadisai da suka zo daga ma'aikin Allah –tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi- a kan haka suna da matukar yawa da fayyace al'amurra a fili da suke nuna irin gatan da musulunci ya yi mace lura da cewa ita mai raunice baibukar taimakoce a koda yaushe  kuma ko wanne iri. An ruwaito cewa wani daga cikin Sahabban ma'aikin Allah –tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi- an sanyashi cikin wadanda za su tafi yaki sai yace medakinshi zata tafi aikin hajji sai ma'aikin Allah –tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi- yace acire sunansa ya tafi ya je ya yi aikin hajji tare da maidakinshi. Kuma wannan al'amarii sannannene cewa alokacin da mace take tare da mahraminta ko mijinta zata dada kamewa doruwa akan wacce take da ita, in kuma ba kamammiya bace to zata kame da izinin Allah, kuma zata zama tana da abokin hira a wannan tafiyar, hikimomi da zaka iya zakulowa cikin muhimmacin mahrami a tare da mace a Halin tafiya ba karamin al'amari bane, duk wanda ya taba yin aikin Hajji zai tabbatar da muhimmancin mahrami tare da mace, ba Mijin-Biza ba domin akwai halin da ake shiga na sai ka rike mata hannu ko jiki, wanda yake haka ba zai yiwuba idan ba maharramaka bace. Malamai sun karawa juna sani kan abinda ya shafi aikin Hajji shin idan aka sami tawaga amintacciya  mace zata iya tafiya a cikinsu ko dab a mahraminta? Sai wannan tawaga ta zama kamar mataimaka a gareta? Malamai da yawa sun tafi akan haka,
          Maganar mahrami maganace da ta taso a aikin Hajjin wannan shekarar ta 1433 Hijira ko 2012 miladiyya, a inda akan hakanne hukumar kasar Saudiya ta dawo da mahajjata mata masu tarin yawa daga kasar, na farko da maganar mahrami tabbatacciiyace a shara'a domin ta fitone daga bakin Ma'aikin Allah –tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi- ba Magana bace da hukumar kasar Saudiya ta kirkiri bam domin na ji Nura Das Ahirarsa da jaridar Leadership Hausa bugu na 313, a shafi na 25 yana cewa Ba kowanne mahajjaci bane ke bin akidar Wahabiyaci, Su a mazahabinsu na Ja'afariyyah wanda aka fi sani Shi'a mace idan ta amincewa kanta ko waliyyanta sun amince mata zata iya tafiya ko inane, wannan Magana tasu ta nuna abinda acewa su Shi'a ba abinda ya hada su da karantarwar ma'aikin Allah, in banda ina maganar bin tafarkin ma'aikin Allah ina kuma maganar wahabiyanci?. Maganar maharami manace data mamaye kafafan yada rabaru a kasarnan kuma maganace da take bukatar a tsaya a yi mata karatun-ta-tsau domin sanin hikimomi da tausayawa da musulunci ya yiwa 'ya mace, kafafan yada labaru sun cancanci yabo yadda suka tunubi malumma akan wannan al'amari wato suka maida al'amarin zuwa ga masu shi. To amma hanzari-ba-gudu-ba maganar da kafofin yada labarai suke yi na cewa anya maganar mahramce kadai tasa wannan al'amari ya faru koko akwai lauje cikin nadi domin mata 'yan Nijeriya kawai aka dawo da su banda 'yan wadansu kasashen? Wannan maganar ya kamata a yi la'akari da ita, wannan ya kaimu abu na biiyu wato.
2. Gurbacewar Tarbiya: A gaskiya Najeriya tana da matukar kima da daraja a idanun kasar Saudiya, amma a gaskiya halayyar da 'yan Najeriya suke nunawa a wadannan wurare masu tsarki musamman ma a birnin Makkah birni mafi tsarki da daraja gaskiya a kwai bantakaici, mata nawane suka tsallake mazajensu su kai zaman dirshan a birnin makkah, me ya kaita? me take yi? Asalin Magana a musulunci mace bata ciyar da kanta kwata-kwata, idan ta yi aure mijinta ya ciyar da ita idan batai aure ba mahaifinta ko waliyyinta ya ciyar da ita. Duk mutumin da ya tabayin aikin hajji zai ga irin halayya da sutura ta rashin mutunci da wasu matan -wasu cikin mahajjata- suke nunawa a ranar sallah matsattsun kaya wasanni marasa kyau tun kafin a gama zaman mina, ballantana a gidan da alhazai suka sauka ka ga yadda ake da 'yan-tuwo-tuwodin abin zai baka mamaki kamar ba a kasa mai tsarki ake ba, idan akai maganar dogon-gida ko Sara-Mansur abirni Makkah da sauran unguwanni kamar su Jabal abin ba'a cewa komai. Ni inagani ya kamata ofishi Najeriya ya shirya wata bita da karantar da 'yan Najeriya da tarbiyantar da su a biranan Makkah da Jiddah da kuma Madina, kuma ya tashi tsaye yaga 'yan Najeriya suna zaune akasar a bisa doka, anan ba ina cewa duka 'yan Najeriya haka suke ba a'a kwata-kwata, akwai tsayayyu, amma mu sani idan fitina ta zo ba tana takaituwa bane ga wadanda suka janyota kamar yadda muka gani a wannan shekarar, zaka iya samun macan da bata ganin jirgin sama a kasaba sai wannan karon amma gashi bala'in wasu ya janyo mata, Allah Madaukakin sarki yana cewa:
          ''Kuma ku ji tsoron fitina wacce ba ta samun danda suka yi zalunci daga cikinku kadai, kuma ku sani lalle ne Allah Mai tsanani ukuba ne'' Sutul-Anfalm aya ta 25.
Mai karatu idan kana jin abinda 'yan Najeriya suke aikata a kasa mai tsarki musamman mata abin zai dauure maka kai matuka da gaske, yanzu idan aka ce maka dukkan matan da suka je Umarar nan data wuce sun dawo nan Najeriya? Me zakace ko kuma ka tambaya.
          Sannan suma hukumar alhazai ta Najeriya ya kamata ta tashi haikan wurin sanyawa maniyyata tsoron Allah da kula da dokokin Sa, a samu malamai masu tsoron Allah wadanda ba himmarsu a biya musu kujeraba, wadannan dakakkun malamai sukasance na dindin-din ko kaso mai yawa daga cikin su sannan abasu damar gudanar da aikin nasu.
3. Mace mai Juna-biyu: Lallekan akwai maganar wahala ga mace mai juna-biyu a aikin hajji mutum ma yana shi kadai ya yacika, amma irin matakin da hukuma ta dauka na haramtawa mace mai juna-biyu aikin hajji wai koda kuwa na wata dayane gaskiya ya kamata a sake duba wannan Magana idan andubeta ta bangaren kiwon lafiya a dubeta ta bangaren addini, babu wani dalili aduk abinda malamai sukai ijima'i aka kafa dalili da shi da ya nuna cewa mace mai juna-biyu bata da damar zuwa aikin hajji, ni ina jin tsoro kada irin wannan hani da aka yiwa wadannan matan yasa aka wannan dayyar matsalar, kada mu sha'afa maganar addini ake yi asalima shi aikin hajjin ginshikine daga cikin shika-shikan musulunci guda biyar, saboda haka kada ka kuskura ka hana wani wannan aiki ba tare da kanada kakkarfan dalili da zaka gabatarwa Allah ba a ranar kiyama, a shekarar da Ma'aikin Allah –Tsira da amincin Allah su kara tabbata a gareshi- Ya yi aikin Hajji wanda shine kuma akekira da hajjin bankwana, adaidai lokacin da Ma'aikin Allah ya isa Zul-Hulaifah inda nan ne mikatin mutanan madina yana zuwa wurin medakin Sayyidina Abubakar ta sauka (tahaihu), kaga kenan ta fito ne ma da tsohon ciki, awannan tafiya da ake akasa ko a doki ko a rakumi, wanda ba za'a hada hakan da jirgin-sama ba ko na ruwa ko mota ba. Wannan matsananciyar dokar data zamar da mata da yawa Hajji Haram ya kamata a sake dubata, wadda ta sanadiyyar ta ake ruwaito mata da yawa suna zubar da cikinsu, irin wannan mataki na anfani da na'urori masu gani harhanji masu ganin-kwakwaf na cewar indai har anbankado cewar tana da ciki to Hajji Haram ya kamata a sake dubawa.
Shawarwari/Mafita: Ni ina ganin bin wadannan shawarwari zai zama wata mafita ga rashin sake maimaituwar irin wannan al'amari, da muke rokon Allah Ya kiyayemu daga maimaituwar wannan alamari:
1.     Tsayawa da tabbatar da mahrami shar'antacce muddin akwai yadda za'a same shi  ba abinda ake cewa mijin-biza ba.
2.     Gabatar da cikakkiyar bita akan mece ''Rifka Ma'amuna'' sannan suwaye, a kuma gabatar musu da bita ta sanin makamar aikin ''Rifka Ma'amuna''.
3.     Tashi tsaye domin a wayar da kan mutane dangane da matsayin mahrami a shara'a, da kuma bayanin gatan da musulunci ya yiwa mata akan sanya musu mahrami da ya yi.
4.     Kimsawa maniyyata tsoron Allah madaukakin sarki, da kuma falalar da maibin Allah yake da ita da kuma narkon sabawa Allah, a gida Najeriya ko a kasa mai tsarki.
5.     Kimsawa maniyyata bin tafarkin Ma'aikin Allah da kuma cewar rabauta duniya da lahira ta tattarune akan tsantsanta biyayya ga reshi.
6.     Karfa halartar maniyyata  wuraran bita.
7.     Samar da wata manhaja ta baidaya kakkarfa akan abinda ya sha fi bita.
8.     Kara samarwa malamai masu tsoron Allah gurabu a harkar hajji, da kuma basu karfin fada aji.
9.     Kara sa ido da dokar da ta dace ga duk wanda ya yi fitsara a duk wurin da ya shafi Hajji tun daga wuraren bita har kamala aikin hajji.
10. Sanya ido ga dukkanin jahar da ta bari wani alhajinta ya ki dawowa.
11. Karamin ofishin jakadancin Najeriya dake birinin Jiddah ya samara da wata ganawa da 'yan Najeriya dake Makkah, Jiddah da Madina domin karantar da su da kuma kara nuna musu tsarkin wurin da suke zaune.
12. Daukar matakin ladabtarwa ga duk dan Najeriyar da ya karya ittifakiyar da aka yi da kasar Saudiyyah.
13. Sake duba maganar mace me juna-biyu, domin kada mu manta tun kafin Saudiya su nemi su zamar da wasu mata Hajji Haram tuni Najeriya ta zamar da wasu.

          Allah madaukakin sarki ya tsaremu ya tsare mana imanimmu, ya kawo mana karshen wannan kiki-kaka da ake yi da alheri, Allah ya kai alhazammu mata da maza kasa mai tsarki lafiya ya kuma dawo mana da su lafiya. Ya Allah katsare mana kasarmu ka zaunar da mu lafiya da dukkanin kasashen musulmi bakiya, amin.
Aliyu Muhammad Sadisu,
 Kwakungu, bayan Ofishin 'Yansanda,
Minna jahar  Neja Nijeriya.
 Za'a iya tuntuba a.
G.S.M. (+234)8064022965.
 e- Imei : aliyusadis@gmail.com
htt:// munbarin-musulunci.blogspot.com
www.fecebook.com/Aliyu Muhammad Sadisu
www.youtube.com/Aliyu Muhammad Sadisu

No comments:

Post a Comment