Wednesday, January 29, 2014

017- TADA IKAMAR SALLAH


Matashiya: Abinda ake nufi da tada ikamar sallah shine: Sanar da wadanda kenan an fara sallah da lafuzza kebantattu. Wannan sai ya nuna mana akwai banbanci tsakaninta da kiran sallah ta fuskoki da dama, daga ciki: Shi kiran sallah sanar da jama'a lokacin sallah ya shiga shi yasa lafuzan kiran sallah suka fi na na ikama yawa, ita ikama ana hadatane da sallah ba'a bukatar jinkiri sabanin kiran sallah shi ana bukatar adan jinkirta saboda jama'a su halarta.
   Tada ikamar sallah al'amarine da ya shafi maza da mata, wato kamar yadda namiji zai tada ikamar sallah lokacin da zai yi sallah to hakama mace zata tada ikama lokacin da zata yi sallah, saidai idan zata bi jam'ine to ikamar da aka tayar ta isar mata, kamar yadda ta isarwa namiji idan shima zai bi sallah ne.
  Muna dada jaddadawa wadannan lafuzza na kiran sallah da ikama koyansu ake yi agaban malami kada mutum yace ya ji ya iya akan titi saboda haka ba sai ya je gaban malam ba.
  Lafuzzan Ikamar Sallah: Lafuzzan tada ikamar sallah sune kamar haka:
اَللهُ أَكْبَرُ، اَللهُ أَكْبَرُ، أَشْهَدُ أَ لاَّ إِلَهَ إِلاَّ اَللهُ، أَشْهَدُ أَنَّ مُحَمَّدًا رَسُولُ اَللهِ، حَيَّ عَلَى اَلصَّلاَةِ، حَيَّ عَلَى اَلْفَلاَحِ، قَدْ قَامَتِ اَلصَّلاَةُ، اَللهُ أَكْبَرُ، اَللهُ أَكْبَرُ، لاَ إِلَهَ إِلاَّ اَللهُ.

Allahu Akbar, Allahu Akabar, Ash'hadu Al Laa'ilaaha Illahu, Ash'hadu Anna Mudammadar Rasulul llahi, Hayya alas Salah, Hayya alal Falah, Qadqamatis Salatu, Allahu Akbaru, Laa'ilaaha illallahu.
Wadannan bayanai malami zai tabbatar maka da ka karanta daidai ko baba karanta daidaiba, ke nan wannan baya wadatarwa sai ka karanta a gaban malami.
  Wadannan lafuzza na kiran sallah da ikama lafuzzane masu girman gaske, sun kunshi tsantsar tauhidi ga Allah madaukakin sarki, da kuma biyayya ga ma'aikin Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi, saboda haka ba'a karawa kuma ba'a ragewa.
   Idan mutum ya yi kiran sallah da lfuzza daidai to batayi ba sai ya sake, haka kuma idan ya yi ikama da lafuzza bibiyu baya yi ba sai ya sake, saidai malamai sun karawa juna sani akan '' Qadqamatis Salatu" wadansu sukace sau biyu za'a yi, wasu kuma sukace saudane, ke nan lafuzza na ibada kiyaye su ake yi kada a kara kuma kada a rage, Allah ya karba mana ibadummu.
Kammalawa: wannan ya nuna mana a fili yadda sallah take da muhimammanci da kuma yadda ta kunshi tsantar lafuzza na kadaita Ubangiji da girmamashi, kuma wannan yake nuna mana cewa ashe komai sai ankoya ba daka ake yiba.
Aliyu Muhammad Sadisu,
 Minna Jahar  Neja, Nijeriya.
 Za'a iya tuntuba a (+234)08064022965,
ko kuma a: e-mail:aliyusadis@gmail.com
Ko a ziyarcemu a yanar gizo, a :
htt:// munbarin-musulunci.blogspot.com   

6 comments:

  1. mashaallah Allah yasaka da alkairi

    ReplyDelete
  2. Enter your comment...Allah Yasa Mudace Da Alkhairi Duniya Da Lahira

    ReplyDelete
  3. Allah Ya Yi maka kyakkyawan sakayya.

    ReplyDelete
  4. Malam Allah Ya saka da alkhari. Tambaya: Ana Hausa ka Allahu Akbar sau daya ake fadi koko sau biyu? Don na ga sau daya aka rubuta shi. Allah Ya biya. Ahmed Daga Gombe

    ReplyDelete
  5. Malam Allah yasaka da gidan Aljanna

    ReplyDelete