Thursday, September 27, 2012

ZIYARA A BIRNIN MADINA


بسم الله الرحمن الرحيم
الحمد لله رب العالمين، والصلاة والسلام على نبينا محمد وعلى آله وصحبه أجمعين
Gabatarwa: Dasunan Allah mai yawam rahama mai yawan jinkai, dukkan godiya ta tabbata a gareshi. Tsira da amincin Allah su kara tabbata ga Annabimmu Annabi Muhammad, da iyalanshi da sahabbanshi baki daya.
          Bayan haka hakika wannan gidauniya ta Annuriyyah ta nema daga gare ni da in kasance cikin wadanda za su gabatarwa da Alhazai bita cikin jerin gwanon abubuwan da yake da alaka da su inda aka fara wannar bita tun ranar lahadin da ta gabata, matashiyar da zan gabatar da jawabi akai itace: Ziyara A Garin Madina. Wanda nake rokon Allah da dukkanin sunayansa mafiya tsarki da siffofinsa mafiya kamala da ya yi mini jagora, ya kuma albarkaci wannan zama namu da wannar gidauniya ya karba mana ayyukammu, amin.
          Wannan jawabi zai tattaru ne akan:
-         Gabatarwa
-         Shinfida
-         Falalar Birnin Madina
-         Ladubban Zama A Birnin Madina
-         Falalar Sallah A Masallacin Ma'aikin Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi)
-         Abubuwan Yi A Birnin Madina
-         Ibadu
-         Wuraren Ziyara Da Takaitaccen Tarihinsu.
Shinfida. Lalle madina wacce take birnine na Ma'aikin Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi) inda kuma take masaukar wahayi inda Ma'ika jibrilu amintaccen Allah ya dinga sassauka ga Manzon Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi), birnin da yake shi ne matattarar imani, mahadar dukkanin wadanda suka yi hijira da wadanda suka tarbesu, hedikwatar musulunci ta farko wanda yake anan ne aka kafa tutar jihadi, daga nan ne kuma aka fita domin a fitar da mutane daga duhu zuwa ga haske, daga nan dinne duniya ta dau haske baki daya, nan ne kuma Allah Madaukakin sarki Ya zabawa Manzan Shi (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi) ya zama wurin hijirarshi, a wannan birni kuma ya rayu, kuma a nan ya koma ga Mahaliccin shi (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi), anan kuma kabarinshi yake wanda yake babu wani mutum da zai iya tabbatar da inda kabarin wani Abbabi yake inbanda kabarin shi (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi). Allah Ya kaimu wannan birni na Ma'aikin shi lafiya, amin.
          A yanzu haka za mu bi wadancan gabobin da suka gabata daya-bayan-daya Allah Ya yi mana jagora, amin.
Falalar Birnin Madina: Hakika wannan birni yana da dunbun daraja da falala wanda yake Allah kadai ya san iyakarsu, ayanzu haka ga kadan daga cikin abinda ya tabbata daga Ma'aikin Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi) na falalar wannan birni:
(1) Allah madaukakin sarki ya sanya shi Harami amintacce kamar yadda ya sanya birinin Makkah harami amintacce, Allah madaukakin sarki yana cewa dangane da birnin Makkah:
Ma'ana: ''Kuma sukace: Har in mukabi gaskiyar dake tare da kai za'a fitar da mu daga kasarmu. Sai Allah yace: Yanzu shin bamu tabbatar musu da wani Harami (na musamman) wanda yake amintacce ba, ana shigo da dukkan nau'ukan 'ya'yan itatuwa wanda yake arzikine daka garemu?, sai dai mafi yawansu ba su sani ba''. (Suratul-Kasas, aya ta:57) Allah madaukakin sarki ya fadi haka a wurare da dama dan gane da Makkah.
    Kuma Ma'aikin Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi) yana cewa dangane da Madina
(( إِنَّ إِبْرَاهِيمَ حَرَّمَ مَكَّةَ، وَإِنِّي حَرَّمْتُ اَلْمَدِينَةَ)) رَوَاهُ مُسْلِم
Ma'ana: Lalle (Annabi) Ibrahim ya haramtar da Makkah, Kuma lalle ni na ramtar da Madina)).
Wannan Hadisi Muslim ne ya ruwaito shi.
(2) Ma'aikin Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi) ya kira wannan birni da suna ''Taibah'' wato daddadan abu, wato kenan birnine mai dadi, mai albarka.
(3) Imani yana tattarewa ya koma wannan birni mai albarka, Ma'aikin Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi) yana cewa :
مُتَّفَقٌ عَلَيْهِ ((   ((إِنَّ اَلإيـمَانَ لَيَأْرَزُ إِلَى اَلْمَدِينَةِ كَمَا تَأْرَزُ اَلْحَيَّةُ إِلَى حُجْرِهَا
Ma'ana: "Lalle Imani yana tattara zuwa madina kamar yadda macijiya take tattara a raminta".
Bukhari da Muslim suka ruwaito.
(4) Birnine da yake haxiye sauran birane. Ma'aikin Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi) ya siffanta ta da cewa garine da yake cinye garuruwa, kamar yadda yake cewa ''An umarceni –da yin hijira zuwa-wani gari da yake cinye garuruwa, suna kiranshi da: Yasriba-wato-Madina'' Bukhari da Muslim suka ruwaito.
             Yasriba shine sunan Madina kafin isar Ma'aikin Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi) da ya isa sai ya canza sunan garin, Allah madaukakin sarki yana cewa –A lokacin da yake fada mana maganar munafuqai aranar Gwalalo.  Ma'ana: Kuma a lokacin da wata tawaga daga cikinsu (su munamukai sukace) Ya ku mutanan Yasriba baku da matsaya ku koma….)
(5) Birnine da Allah ya zabeshi ya zama wurin hijirar manzonshi (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi).
(6) Yadda ma'aikin Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi) ya nuna darajarta da girman sabawa Allah a cikinta, Ma'aikin Allah yana cewa:
((اَلْمَدِينَةُ حَرَمٌ مَا بَيْنَ عَيْرٍ إِلَى ثَوْرٍ، مَنْ أَحْدَثَ فِيهَا حَدَثًا أَوْ آوَى مُحْدِثًا فَعَلَيْهِ لَعْنَةُ اَللهِ وَالْمَلاَئِكَةِ وَالنَّاسِ أَجْمَعِينَ))                                   رَوَاهُ اَلْبُخَارِيُّ وَمُسْلِم.
Ma'ana: Madina Haramce daga (Dutsan) Air zuwa (Dutsan) Saur, duk wanda ya aikata barna a cikinta ko ya baiwa mabarnaci mafaka Tsinuwar Allah ta tabbata a kanshi da Mala'iku da mutane baki daya''                    Bukhari da Muslim.
(7) Addu'ar Albarka. Yana daga cikin falalar wannan birni addu'ar albarka da ya samu daga ma'aikin Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi), ma'aikin Allah yana cewa:
اَللَّهُمَّ بَارِكْ لَنَا فِي ثَمَرِنَا، وَبَارِكْ لَنَا فِي مَدِينَتِنَا، وَبَارِكْ لَنَا فِي صَاعِنَا، وَبَارِكْ لَنَا فِي مُدِّنَا)) مسلم
Ma'ana ''Ya Allah ka sanya mana albarka a 'ya'yan itatuwammu, ka sanya mana albarka a Madinarmu, ka sanya mana albarka a Sa'immu, ka sanya mana albarka a mudummu''  
                                                                    Muslinme ya ruwaito.
(8) Annoba da Julal basa shiga madina. Ma'aikin Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi) yana cewa:
''Mala'ikune akan ganuwowin madina Annoba bata shigarta haka namma Jujal''  Bukhari da Muslim.
      Wannan kadan kenan dangane da birnin madina banda abinda ya gabata tun a shinfida, sabo da lokaci.
Ladubban Zama A Madina: Lalle duk wanda Allah ya kaddari cewa yana cikin wadanda za su zauna kwana ko awanni a cikin wannan birni mai albarka to lalle ya sani cewa wannan ba karamar falala bace da Allah ya yi masa, sabo da haka sai ya godewa Allah akan wannan falalar, ya kuma kula da ladubban zama a wannan birni mai daraja kamar haka:
(1) Ka so wannan gari sabo da falalar da yake da ita, da son da ma'aikin Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi) yake masa.
     Anas Ibnu Malik (Allah Ya Kara mishi yarda) yana cewa ''Lalle ma'aikin Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi) ya kasance idan ya dawo daga tafiya sai ya hango gine-ginen madina sai ya gyara abin zamansa, in kuma yana kan dabbane sai ya motsa ta, Saboda son da yake mata (wato madina).
(2) Ka kwadaitu da tsayuwa a kan al'amarin Allah, ka zama mai lizimtar biyayyah ga Allah da manzan Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi), kana mai tsananin kaucewa sabon Allah da bidi'oi domin wadannan al'murra yinsu a harami ba karamin zunubi bane.
(3) Lizimtar Sallah a cikin masallacin Ma'aikin Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi) kamar yadda bayani zai zo.
(4) Ka zama kyakkyawan abin koyi, domin fa kana inda daga nanne hasken ya haskaka duniya baki daya.
(5) Ka tuna fa kana inda nanne masaukar wahayi, kuma inda Allah ya zabawa manzanshi ya zame masa wurin hijira, kana inda yake nanne matattarar imani, kana inda nance makarantar da sahabban ma'aikin Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi) su kai karatu kada kai wani aiki da ya sabawa na makarantarsu da malaminsu (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi).
(6) Kada kaga tsuntuwa ka dauka sai dai idan zakai cigiya.
Falalar Sallah A Masallacin Ma'aikin Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi).
      Hakika sallah a wannan masallaci da wannan Annabi ya gina tana da matukar falala wacce bai kamata wanda ya sami kanshi a inda wannan masallaci yake ba ya yi sakaci, hadisai tabbatattu sun yi bayanin matsayin wannan masallaci da matsayin sallah a cikin shi. Na farko dai wannan masallaci yana cikin masallatai uku da ake nikar gari domin ziyartar su, kamar yadda Ma'aikin Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi) yake cewa a hadisin Bukhari da Muslim.
((لاَ تُشَدُّ اَلرِّحَالُ إِلاَّ إِلَى ثَلاَثَةِ مَسَاجِدَ: اَلْمَسْجِدِ اَلْحَرَامِ، وَمَسْجِدِي هَذَا، وَالْمَسْجِدِ اَلأَقْصَى)) متفق عليه
Ma'ana: ''Ba'a nikar gari (don ziyara) sai masallatai uku; Masallaci mai alfarma (dake makka), da kuma wannan masallacin nawa, (dake birnin madina) da kuma masallacin can nesa (wandake Kudus).   Bukhari da Muslim.
    Abinda Ya Shafi Falalar Sallah a wannan masallacin ma'aikin Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi) yana cewa;
((صَلاَةٌ فِي مَسْجِدِي هَذَا أَفْضَلُ مِنْ أَلْفِ صَلاَةٍ فِيمَا سِوَاهُ إِلاَّ اَلْمَسْجِدَ اَلْحَرَامَ)) متفق عليه
''Yin Sallah a cikin masallacin nan nawa ya fi salloli dubu a (masallacin) da ba shi ba in banda masallacin harami (Makka)'' Bukhari da Muslim.
 Lalle wannan ba karamar garabasa bace da rahamar Allah ga bayinsa, kuma yana da kyau mu fahimci abubuwa kamar haka:
a.     Wannan ninkin ladan da abinda yafi dubu ba wai ya takaitu da farilla bane banda nafila, ko ko nafila banda farilla, a'a ya shafi duka, raka'a biyu ta farilla acikinsa ta fi raka'oi dubu na farilla a inda ba shiba in banda haramin makkah, raka'a biyu ta nafila sun fi raka'o'i dubu na nafila a inda ba nan ba.
b.    Wannan ladan bawai ya takaitu a iya inda masallacin yake a lokacin ma'aikin Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi) kawai bane ya shafi har fadadashin da aka yi ne.
c.     Sai dai duk wanda yabi sallah a wajan masallaci yana da ladan jam'i amma baida wancan ladan da aka anbata domin a waje ya yi sallah ba a ciki ba. Anan nake cewa irin sakacin da ake na a zauna a waje aita fira ko aje a sayo kaya niki-niki jami'ai su hana a shiga masallaci da shi mutum ya yi sallah a waje bakaramar asara bace.
d.    A cikin masallacin akwai wani wuri wato Raudha, Ma'aikin Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi) a hadisin Bukhari da Muslim ya siffanta wurin da cewa Dausayine daga cikin dausayin aljanna. Kebance wannan wuri da irin wannan siffa lalle ya nuna falalarsa doruwa akan sauran wuraren.
Abubuwan Yi A Birnin Madina: Lalle ilalla a yanzu kasan takaitaccan bayani dangane da birnin madaina falalar birnin da ladubban zama a birnin. To yanzu idan Allah ya sa ka isa wannan birni menene abinyi kada ka manta tafiyarka ba tafiyar bude ido bace. Saboda haka babban abinda ya kaika shine ziyarar wannan masallaci da wannan Annabi cikamakin Annabawa farin jakada ya gina da hannayanshi masu albarka, sabo dahaka kada hankalinka ya dauku daga barin salloli da karatun alkur'ani da zikiri a cikin wannan masallaci, domin duk ibadar da ka gudanar a cikin wannan masallaci ladanta ya nin-ninka wacce aka yi a wajan wannan masallaci inbanda masallaci Ka'abah.
     Sannan yanzu bari a kawo abinda ake yi a birnin madina:
Ibadu. Idan akace ibadu to jam'ine na ibada ita kuma ibada  ''Gamamman sunane da ya tara dukkan abinda Allah yake so kuma ya yarda da shi na ayyuka ko na Magana na zahiri ko na baxini''
          Yanzu munsan mecece ibada, kuma lura da ta'arifin ta lalle munsan tanada nau'i daban-daban, kadan daga ciki sune:
(1) Ikhlasi: Yi domin Allah,  kada ka kuskura ka yi wani aiki a wannan birni mai tarin albarka wanda yake badon Allah ba ko Allah bai saka ba, lalle mutum zai yi asara, ba'a lissafawa Allah ayyuka ko ayi mishi gori wadannan suna lalata ayyuka.
(2) Salloli A Kan Lokaci: Lalle wanda ya sami kanshi a wannan birni mai albarka kada ya kuskura ya sake da sallah, to yanzu wanda ya yi sake da sallah a inda aka saukar da sallar to a inane ba zai yi sake da itaba, musamman a cikin wannan masallaci maitarin albarka.
(3) Yawaita Karatun Alkur'ani: anan ba wai sai ka haddace ba ko ka sauka a'a iya inda ka iya ka nace da karanta shi, wannan ba karamin alkhairi bane.
(4) Yawaita Zikiri, Istighfari, Salatin Annabi (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi) Zikiran safe  da na yamma, kada ka manta saboda wadannan al'amura kabar kasarka, wurin aikinka, ka rufe shagonka kada mutum ya yi wasa da wadannan ayyuka musamman a cikin wannan masallaci da ake nunnunka ayyuka.
(5) Taimakon Juna: Lalle kada zuciyarmu ta yi nesa da taimakawa juna abune mai mahimmanci tabangaren guzuri shawara nasiha ga juna, zaburar da juna, neman …''
Wuraren Ziyara Da Takaitaccan Tarihinsu: Yana dakyau mu tsaya mu yi karatun ta-natsu a kan abinda ya shafi ziyara a makka ko a madina kada harkar ziyara tasa ka rasa sallah a cikin wadannan masallatai wadanda suke sune jigo uban-tafiya. Yanzu za'a lissafo wuraren ziyara, kamar haka:
(1) Masallacin Ma'aikin Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi). Wannan masallaci ma'aikin Allah Ya sayi filin wurinne da kudinsa sannan ya aza harsashin gininshi da hannayen sa masu albarka, masallacin ya zama nanne wurin sallah nanne kuma makaranta inda yake karantarwa kuma ananne yake alqalanci (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi), anan yake tarbar baqinshi.
  Yadda Ake Ziyara a wannan masallaci shi ne, dazarar kun isa madina ankaiku masauki kowa ya aje kayansa sai a nufi wannan masallaci maialbarka idan akaje sai afara gabatar da kafar dama lokacin shiga, sai kai addu'a kace:
بِسْمِ اَللهِ، وَالصَّلاَةُ وَالسَّلاَمُ عَلَى رَسُولِ اَللهِ، اَللَّهُمَّ اَفْتَحْ لِي أَبْوَابَ رَحْمَتِكَ
Sannan sai ka yi sallah raka'a biyu, idan ka tarar ana farilla sai kabi ta wadatar maka, idan kuma ka isa an idar da sallah  sai ka yi farillar.
(2)  Kabarin Ma'aikin Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi) Da manyan sahabbanshi biyu: wadannan kabarurruka suna cikin dakin sayyida Aisha ne –Allah ya kara mata yarda- kamar yadda kowa ya sani ne masallacin ma'aikin Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi) daban yake dakunan iyalanshi ma daban suke wato gini ya rabasu, bayan da Allah ya karbi yaruwar wannan Annabi mai daraja a dakin Sayyida Aisha sai aka yi masa kabari a dakin, haka kuma wadannan manyan sahabbai nashi guda biyu wadanda zaka ji yana cewa na kasance ni da Abubakar da Umar na yi  kaza ni da Abubakar da Umar, Allah ya kara musu daukaka da karamci da kuma yarda, amin.
     Yadda Ake Ziyara anan mutum zaizo ta gaba sai ya fuskanci qabarin Ma'aikin Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi) sai yace:
اَلسَّلاَمُ عَلَيْكَ يَا رَسُولَ اَللهِ وَرَحْمَةُ اَللهِ وَبَرَكَاتُهُ صَلَّى اَللهُ وَسَلَّمَ وَبَارَكَ عَلَيْكَ، وَجَزَاكَ أَفْضَلَ مَا جَزَى نَبِيَّا عَنْ أُمَّتِهِ.
Ma'ana: Amincin Allah ya tabbata a gareka ya ma'aikin Allah da rahamarsa da albarkarsa, Allah ya kara maka salati da aminci da kuma albarka, ya sakanka maka da mafificin abinda ya sakankawa wani Annabi dangane da al'ummarsa.
Mutum zai yi hakane ba tare da daga murya ba, domin ba'a daga wa ma'aikin Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi) murya yana da rai ko bayan ya rasu, ka duba Suratil-Hujrat aya ta (2-3).
Sannan sai ya dan yi dama kadan sai yace:
اَلسَّلاَمُ عَلَيْكَ يَا أَبَا بَكْرِ اَلصِّدِّيقَ
Ma'ana: Amincin Allah ya tabbata a gareka ya Abubakar maigaskiya.
sannan sai ya danyi dama kadan, sai yace:
اَلسَّلاَمُ عَلَيْكَ يَا أَبَا حَفْصٍ عُمَرَ اَلْفَارُوقَ
Ma'ana: Amincin Allah ya tabbata a gareka ya wannan gwarzo Umar.
Sai mutum ya yi musu adda'a domin sun yiwa wannan addini hidima da duk abinda za su iya, Allah ya kara musu daukaka.
(3) Makabartar Baki'a: ita wannan kushewa bata da nisa da masallacin ma'aikin Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi) bai wuce taku kadan ba, itace babbar kushewar madina nan aka binne su Nana Aisha da Nana Fafima da Sayyina Usman da manya-manyan sahabban ma'aikin Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi), nan kuma aka binne su Imamu Malik, Allah ya kara musu yarda, amin.
   Idan mutum yaje wannan makabarta zaicene :
اَلسَّلاَمُ عَلَيْكُمْ دَارَ قَوْمٍ مُؤْمِنِينَ وَإِنَّا إِنْ شَاءَ اَللهُ بِكُمْ لاَحِقُونَ، يَغْفِرُ اَللهُ لَنَا وَلَكُمْ
Ma'ana: Amincin Allah ya tabbata a gareku ya mutanan wannan gida da suke muminai, muma in Allah ya yarda munanan zamu tarar da ku, Allah ya gafartama ya gafarta muku.
(4) Shuhada'u Uhud: Kushewar shahidan Uhudu kushewace dake dab da dutsan Uhudu, anan ne aka yiwa sahabban ma'aikin Allah wadanda suka yi shahada a wannan yaki mai cike da darussa janaza, wanna a cikinsu akwai Sayyidina Hamza wanda Allah yaba da labarinsa a cikin suratul Ali-Imrana.
  Siffar yadda ake ziyara anan itace irin yadda aka yi a baki'a, wato idan kaje makabartar sai kace:
اَلسَّلاَمُ عَلَيْكُمْ دَارَ قَوْمٍ مُؤْمِنِينَ وَإِنَّا إِنْ شَاءَ اَللهُ بِكُمْ لاَحِقُونَ، يَغْفِرُ اَللهُ لَنَا وَلَكُمْ
Ma'ana: Amincin Allah ya tabbata a gareku ya mutanan wannan gida da suke muminai, muma in Allah ya yarda munanan zamu tarar da ku, Allah ya gafartama ya gafarta muku.
(5) Masallacin Kuba: Wannan shine masallacin da ma'aikin Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi) ya gina kafin ya shiga birnin madina, domin ya yi kwanaki anan kafin ya shiga, anan ne kuma ya yi sallar juma'a ta  farko a musulunci.
 Falalar Masallacin Kuba: wannan masallci yana da falala ta musamman da ma'aikin Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi) ya bayya, Abdullahi dan Umar (Allah ya kara masa yarda) yace: ''Ma'aikin Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi) ya kasance yana zuwa masallacin Kuba a duk ranar asabar wani lokacin ya tafi a kafa wani lokacin kuma ya hau abin hawa sai ya yi sallah raka'a biyu''                                                               Bukhari da Muslim.
  Hakanan ankarbo daga Sahal dan Hunaif (Allah Ya kara masa yarda) yace Ma'aikin Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi) yace:
           ''Duk wanda ya yi tsarki daga gidanshi sannan ya je (masallacin) Kuba ya yi sallah a cikin shi to ya kasance yana da ladan Umarah''  Ibnu Majah da wasu suka ruwaito.
           Wadannan sune wuraran ziyara shar'antattu su biyar (5), biyu masallatai (Masallacin Ma'aikin Allah (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi) da masallacin Kuba), uku makabartu.
          Amma akwai wasu wurare da mutane suke zuwa da sunan ziyara wadannan wurare sun kasu kashi biyu:
(1)            Akwaishi A Tarihi: Kamar kiblatai, wannan a kwai shi a tarihi sai dai masallacin da ake kira kiblataini a yau shine wanda tarihin ya nuna ? to wannan malamai masana Sira da Tarihi sun karawa juna sani akan haka.
(2)            Babu Shi A Tarihi: a kwai wuraren da suke inda zaka karade littafai dakyar ka ji duriyarsu domin babu su, an same su ne a zamanin wadansu dauloli da suka wuce.
Shawarwari:
Ni ina gabatar da nasiha ga 'yan-uwa kamar haka:
1.    Rikon abinda ya kaika.
2.    Kada ka dauki wannan tafiya a matsayin yawon bude ido.
3.    Lizimtar Ibada a wadannan masallatai.
4.    Sanya lokacin ziyara ya kasance da safe, domin kada ka rasa sallah a masallacin ma'aiki (Tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi).
5.    Kimanta lokaci.
6.    Abokantaka da wanda yake da himma.
7.    Barin shiga kasuwa sai an idar da sallar isha.
8.    Daraja wannan wuri domin Allah ya daraja shi
9.    Ba'a dawafi a madina domin a ka'aba kawai ake dawafi, kamar yadda ya fada a Suratul-Hajj
Kira ga wannan gidauniya  da ta ci gaba da gudanar da irin wannan bita, da fatan Allah ya sanya mata albarka, ya kuma karbi ayyukammu.
وصلى الله وسلم على نبينا محمد وعلى آله وصحبه وسلم
Aliyu Muhammad Sadisu,
 Kwakungu, bayan Ofishin 'Yansanda,
Minna jahar  Neja Nijeriya.
 Za'a iya tuntuba a.
G.S.M. (+234)8064022965.
 e- Imei : aliyusadis@gmail.com
htt:// munbarin-musulunci.blogspot.com
www.fecebook.com/Aliyu Muhammad Sadisu

18 comments:

  1. Question about clipping nails during menses?
    Is it permissible for a woman to clip her nails during menses?This is a matter concerning which many women are confused, namely the ruling on removing hair and nails and other Sunnahs of the fitrah during the menstrual period. This stems from a false belief that some of them have, that all parts of a person will come back to him on the Day of Resurrection, so if he removes them when he is in a state of major impurity due to janaabah, menses or post-partum bleeding, they will come back to him impure (naajis) and not purified (taahir) on the Day of Resurrection. This is a false notion and an illusion which is not correct at all.

    ReplyDelete
  2. webstorm crack Thanks for this post, I really found this very helpful. And blog about best time to post on cuber law is very useful.

    ReplyDelete
  3. utorrent pro crack Thanks for sharing such great information, I highly appreciate your hard-working skills which are quite beneficial for me.

    ReplyDelete
  4. nordvpn-crack-full-version is pricing quite reasonably. Even when you're on a budget, then it is easily affordable. Certainly, NordVPN now offers the very best value available on the current marketplace, particularly if you're searching for lasting support using premium features.
    new crack

    ReplyDelete
  5. Thanks for the post. Very interesting post. This is my first-time visit here. I found so many interesting stuff in your blog. Keep posting.. smartdraw-crack

    ReplyDelete
  6. https://munbarin-musulunci.blogspot.com/2012/09/ziyara-birnin-madina.html?showComment=1538185281156#c8505397246213908888

    ReplyDelete
  7. This design is wicked! You most certainly know how to keep a reader amused.
    Between your wit and your videos, I was almost moved to start my own blog (well, almost…HaHa!) Great job.
    I really loved what you had to say, and more than that, how you presented it.
    Too cool!
    norton utilities activation code free
    adguard serial key
    araxis merge serial number
    1click dvd copy pro free download
    bitwig crack
    Crack Like

    ReplyDelete
  8. Your hard work has not gone unnoticed. I and the entire senior management would like to congratulate you on doing a great job.
    kaspersky anti virus crack
    norton internet security crack
    zonealarm antivirus crack

    ReplyDelete
  9. Your website is fantastic. The colors and theme are fantastic.
    Are you the one who created this website? Please respond as soon as possible because I'd like to start working on my project.
    I'm starting my blog and I'm curious as to where you got this from or what theme you're using.
    Thank you very much!
    musicbrainz picard crack
    pcdj dex crack
    activatorsqlite expert personal
    corelcad crack

    ReplyDelete
  10. Windows 7 Professional Crack creates more unequivocal photographs and makes games, video web based, and media altering smoother. You can likewise appreciate more clear, more excellent sound through the refreshed sound driver.

    ReplyDelete
  11. Great ! I appreciate your consideration guidance, help, time.
    PAYDAY 2 Crack
    goodsync crack

    ReplyDelete
  12. Thank you for helping people get the information they need. Great stuff as usual. Keep up the great work!
    Ori and the Will of the Wisps Crack
    traktor pro crack

    ReplyDelete
  13. Outstanding Blog, Thanks for sharing this Amazing information. Very helpful for me. Asian Drama,
    pinstripe crack
    jump king crack
    The Settlers Crack

    ReplyDelete
  14. I guess I am the only one who came here to share my very own experience. Guess what
    I am using my laptop for almost the past 2 years, but I had no idea of solving some basic issues.
    I do not know how to Crackadvise Free Download But thankfully, I recently visited a website named Crackadvise.Crack

    Corel VideoStudio Crack

    SoftPerfect Network Scanner Crack

    Aeesoft Buisrnova Crack

    Nero Burning ROM Crack

    VMware Fusion Pro Crack

    Arclab Watermark Studio Crack

    ReplyDelete
  15. Nice article and explanation Keep continuing to write an article like this you may also check my website Crack Softwares Download We established Allywebsite in order to Create Long-Term Relationships with Our Community & Inspire Happiness and Positivity we been around since 2015 helping our people get more knowledge in building website so welcome aboard the ship.

    reloader-activator-crack

    sparkol-videoscribe-crack

    spotify-premium-crack

    ReplyDelete



  16. Nice article and explanation Keep continuing to write an article like this you may also check my website Crack Softwares Download We established Allywebsite in order to Create Long-Term Relationships with Our Community & Inspire Happiness and Positivity we been around since 2015 helping our people get more knowledge in building website so welcome aboard the ship.

    nova-launcher-prime-apk crack

    rhinoceros-crack-license-keygen crack

    sony-vegas-pro-crack

    ReplyDelete